'Yan tawayen M23 da gwamnatin Rwandan ke mara wa baya, - da suka karbe daukacin gabashin jamuriyar Dimukradiyyar Congo - sun ce za su ci gaba da dannawa har sai sun cimma nasara, bayan karbe iko da kudancin Kivu a jiya Juma'a.
Mayaƙan na M23 sun kuma kwace iko da babban filin jirgin saman Bukavu.
Ƴantawayen na M23 sun karɓe iko da birnin Bukavu, mai al'umma kusan miliyan guda.
Hakan ne kuma ya bai wa M23 damar karɓe iko da tafkin Kivu da kewaye. \
A watan da ya gabata ne suka karɓe birnin Goma mai muhimmanci, lamarin da ya MDD ta ce sama da mutum 3000 ne suka mutu, wasu dubban farar hula sun rasa muhallansu.
Shugaban Congo ya zargi gwamnatin Rwanda da taimaka wa 'yan tawayen M23, zargin da Kigali ta sha musantawa.
Ana sa ran batun tashin hankalin na Congo da Sudan, su za su mamaye taron ƙasashen Afurka da ke gudana a birnin Addis Ababa na ƙasar Habasha.