Isra'ila ta kori mutane daga asibiti ɗaya tilo da ya rage a arewacin Gaza
An rufe asibiti ɗaya tilo da ya rage a arewacin Gaza, bayan dakarun Isra'ila sun bayar da umarnin a fice daga cikin sa da gaggawa.
Shugaban asibitin Dr Mohammed Salha ya ce an kwashe jama'a daga asibitin Al-Awda da ke Jabalia a ranar Alhamis da yammaci.
Ya shaidawa BBC cewa "Muna cikin takaici matuƙa saboda tilasta rufe asibitin, bayan kutse na makonni biyu da aka yi. A yanzu dai wannan na nufin babu sauran asibiti a arewaci.''
Isra'ila ba ta ce komai ba a kai, kuma BBC ta tuntuɓi rundunar sojin Isra'ilan.
Dr Salha ya tabbatarwa BBC cewa an yi ruwan bama-bamai da harsasai a kan asibitin a ranar Alhamis, kuma dakarun Isra'ilan ne suka yi.
Ya ce yana cikin asibitin ne kuma dakarun Isra'ilan suka kira shi tare da bayar da umarnin kowa ya fice daga asibitin cikin gaggawa.
Hukumomin lafiya na duniya sun yi Allah wadai da matakin.