Arsenal za ta karɓi bakuncin Manchester City a wasan mako na biyar a Premier League ranar Lahadi.
Arsenal tana mataki na uku a teburin babbar gasar tamaula ta Ingila da maki, tara, bayan cin wasa uku da rashin nasara ɗaya.
Ita kuwa City tana ta maki 11 da maki shida, bayan nasara biyu aka doke ta wasa biyu.
A bara da suka fuskanci juna sun tashi 2-2 a Etihad, sai Arsenal ta sharara 5-1 a ragar City a wasa na biyu a Emirates a Premier League.
Kenan Gunners na fatan doke City karo na biyu a jere a karon farko tun bayan Disambar 2015.
Kungiyar Emirates ta lashe dukkan wasa ukun da ta buga a gida a bana da cin wallo 9-0.
Rabon da ta yi nasara huɗu a jere a gida ba tare da an zura mata ƙwallo ba a raga a Premier tun Disambar 2021.
City ta yi rashin nasara biyar daga wasa bakwai da zarar ta buga gasar zakarun Turai a tsakiyar mako.
Pep Guariola ya yi rashin nasara huɗu a Premier League a wasa da Arsenal, watakila ya zama karo na biyar ba zai doke Arsenal ba - kenan Mikel Arteta zai zama kociya na farko da zai yi wasa biyar a kan Guradiola ba tare da rashin nasara ba.
Sai dai Haaland ya ci Arsenal ƙwallo huɗu daga wasa shida da ya fuskanci ƙungiyar a Premier League, sannan ya zura ƙwallo 19 a raga a wasa 20 da suka kai ziyara Landan.