Ƙasashen Afirka sun nemi Iran da Isra'ila su kai zuciya nesa

Asalin hoton, Reuters
Ƙasashen Afirka da dama sun yi kira ga Isra'ila ta kai zuciya nesa yayin da kwamitin shirya yaƙinta ke tattaunawa domin yanke hukuncin ko za su kai harin ramuwar gayya sakamakon harin ba-zata da Iran ta kai mata ranar Asabar da daddare.
Iran ta ce ta kai harin ne a matsayin martani ga hari ta sama da Isra'ila ta kai kan ofishin jakadancinta da ke Damascus ranar 1 ga watan Afrilu wanda ya kashe mata dakarun juyin juya hali.
Iran ta kai hari da fiye da jirage marasa matuƙa 300 da makamai masu linzami - galibinsu kuma an daƙile su kamar yadda sojojin Isra'ila suka bayyana.
Najeriya da Kenya da Afirka ta Kudu da Somalia ƙasashen Afirka ne da suka yi kiran a kai zuciya nesa domin hana ɓarkewar yaƙi.
Cikin wata sanarwa, sashen da ke kula da haɗin kai da alaƙar ƙasashen waje a Afirka ta Kudu ya ce "dole ne duka ɓangarorin su danne zuciyarsu sannan su guji matakin da zai janyo tashin hankali musamman a yankin da ke fama da rikici".
Shugaban Kenya, William Ruto ya buƙaci Isra'ila ta yi haƙuri ganin buƙatar duka ɓangarorin su kaucewa tsunduma yaƙi da za a yi wuyar farfaɗowa."
Ya ce harin da Iran ta kai ya nuna barazana ga tsaro da zaman lafiyar duniya.
Somaliya ta yi kira ga al'ummar duniya da su ɗauki mataki na sassauta rikicin tare da rage haɗarin faɗa wa tashin hankali."
Ma'aikatar harkokin wajen Najeriya ta yi kira ga Isra'ila da Iran da su yi tunani kan alƙawarinsu ga ƙudurorin zaman lafiya".
Iran da Isra'ila ba su da wata alaƙar siyasa mai zurfi a yankin kudu da hamadar Sahara.
- Hankalin duniya ya karkata kan martanin da Isra'ila za ta mayar wa Iran




