Aisha Adam Hussaini ce ta lashe gasar Hikayata ta BBC Hausa, 2023

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

A'isha Babangida, Mukhtar Adamu Bawa, Abdullahi Bello Diginza and Haruna Kakangi

  1. Sojojin Isra'ila sun ce za a ci gaba da tsagaita buɗe wuta a Gaza

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Sojin Isra'ila sun sanar da tsawaita yarjejeniyar tsagaita wuta a yakin Gaza da ƙarin kwana guda, daidai lokacin da masu shiga tsakani ke kokarin ganin an sako karin wadanda bangarorin biyu ke tsare da su.

    Isra'ilawa 12 da 'yan Thailand 4 da mayaƙan Hamas ke tsare da su a Zirin Gaza, da kuma suka samu 'yanci a jiya Laraba sun isa Isra'ila.

    Ita ma Isra'ila ta saki Falasdinawa mata da kananan yara 30 da ta ke tsare da su agidajen kasonta.

    Majiyar FalasƊinawa na cewa za a Ƙara tsawaita tsagaita wutar da kwanaki 4, yayin da majiyar Isra'ila ke cewa da kwanaki 2.

    Sakataren harkokin wajen Amirka Antony Blinken na Tel Aviv domin bukatar kara wa'adin.

    • Yadda Hamas ta haɗa dakarun da suka kai wa Isra'ila harin 7 ga Oktoba
    • Abin da ya kamata ku sani kan yarjejeniyar Isra'ila da Hamas
  2. Assalamu Alaikum

    Masu bibiyar mu barkan mu da war haka.

    Barkan ku da sake kasancewa da mu a shafin kai tsaye na BBC Hausa

    Aisha Babangida ce za ta kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabtanta da kuma sauran sassan duniya.