An zaɓi Najeriya cikin ƙasashen da za su nemo mafita kan rikicin Gaza

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najieriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

A'isha Babangida, Haruna Kakangi, Mukhtar Adamu Bawa and Ahmad Tijjani Bawage

  1. Amurka za ta dawo da kai agajin abinci a Habasha

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Amurka ta ce za ta ci gaba da kai kayan agajin abinci a faɗin ƙasar Habasha a watan Disamba, watanni shida bayan dakatar da su bisa zargin cin hanci da rashawa.

    Hukumar ci gaban ƙasashen duniya ta Amurka (USAid) ta ce gagarumin garambawul zai tabbatar da cewa kayan abinci sun kai ga waɗanda suka fi buƙata.

    Sake dawo da tallafin zai kasance a kan gwaji na shekara guda, in ji hukumar.

    Miliyoyin mutanen Habasha na fuskantar ƙarancin abinci saboda illar tashe-tashen hankula da tsananin yanayi.

    Amurka ta dakatar da bayar da agaji a watan Yuni, inda ta yi ƙorafin yadda ake karkatar da kayayyakin tare da hadin gwiwa.

    • Anya tallafi na kaiwa ga 'yan Ethiopia kuwa?
    • Yakin Ethiopia da Tigray: Labarin birnin Mekelle da aka raba da sauran duniya
  2. Shugaban China da na Amurka za su gana a yau

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaban China da na Amurka na San Francisco inda za su yi ganawar keke-da-keke a karon farko cikin shekara guda.

    Shugaba Biden ya ce yana fatan takwaransa Xi Jinping zai taimaka wajen ganin an inganta alaƙa tsakaninsu.

    Tun bayan wata ziyara da shugaban China ya kai Amurka a cikin shekara ta 2017, ƙasashen biyu ke ta tafka rikicin kasuwanci da kuma rashin jituwa kan batutuwa da dama, kama daga tsaro har zuwa hakkin bil'adama.

    Ana dai ta raɗe-raɗin cewa ganawarsu ta yau Laraba za ta iya dawo da ko inganta ayyukan soji tsakanin ƙasashen.

    • Yadda Amurka ke son ƙulla ƙawance da makwaftan China
    • Ko China za ta iya kere Amurka a fagen ƙirƙirarriyar basira ta AI?
  3. Sojojin Isra'ila sun kai samame a babban asibitin Gaza

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Sojojin Isra'ila sun kai samame kan wani ɓangare na asibiti mafi girma Al-Shifa da ke Zirrin Gaza.

    Sojojin sun bayyana cewa wannan samame a kan asibitin Al-Shifa wani bangare ne na farautar mayaƙan Hamas.

    A lokacin da BBC ya tuntubi wani ganau a asibitin ya shaida masa yadda sojoji suka nufi asibitin da jeren motoci masu sulke, kuma adadin waɗanda suka farwa ɓangaren bada kulawar gaggawa sun haura sojoji 100.

    Isra'ila na zargin Hamas da amfani da wannan cibiya wajen kitsawa da kuma kai hare-hare.

    A jiya Talata Amurka ta fito tana cewa ta tattara bayanan sirri da ke tabbatar da iƙirarin Hamas.

    Hamas dai na cewa kalaman Amurka karfafa gwiwa ne ga sojojin Isra'ila na cigaba da kai hare-hare Gaza.

    • WHO ta ce ayyuka sun tsaya cak a babban asibitin Gaza
    • Sojojin Isra’ila sun amince su kwashe jarirai daga babban asibitin Gaza
  4. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da safiyar Laraba tare da fatan kun shigo shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa lafiya.

    Aisha Babangida ce za ta kawo muku rahotanni daga sassan duniya, musamman game da halin da ake ciki a hare-haren da Isra'la ke kai wa Zirin Gaza da kuma martanin mayaƙan Hamas a kan ƙasar.