Hukumomi sun sanya dokar hana fita a Kano

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

A'isha Babangida, Haruna Kakangi, Abdullahi Bello Diginza and Mukhtar Adamu Bawa

  1. An cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a yankin Nagorno-Karabakh

    ...

    Asalin hoton, ARTSAKH PUBLIC TV

    Kwana guda bayan da sojojin Azerbaijan suka ƙaddamar da farmaki a yankin Nagorno-Karabakh, mayaƙan Armenia sun amince da wasu shawarwarin da Rasha ta bayar na tsagaita wuta.

    Ɗaya daga cikin mahimman buƙatun da dakarun Karabakh suka amince da shi, shi ne shawarar kwance ɗamara gaba ɗaya.

    Armeniyawa kimanin 120,000 ne ke zaune a yankin Kudancin Caucasus, wanda aka amince da shi a matsayin wani yanki na Azerbaijan.

    Shekaru uku da suka gabata, Azerbaijan ta sake kwace wasu yankuna a ciki da kuma kewayen yankin Karabakh, kuma a ranar Talata ta buƙaci miƙa wuya baki ɗaya.

    Jami’an Karabakh sun ce aƙalla mutum 27 ne suka mutu, wasu 200 kuma suka samu raunuka tun bayan da sojojin Azerbaijan suka ƙaddamar da wani abin da suka kira yaƙi da ta’addanci.

    Fadar shugaban kasar Azerbaijan dai ta ce jami'ai za su gana da wakilan Karabakh na Armenia domin tattaunawa kan "batun sake hadewa" a garin Yevlakh na Azerbaijan a ranar Alhamis.

    Garin yana da nisan kilomita 100 daga arewacin Karabakh, babban birnin yankin Khankendi, wanda Armeniyawa suka fi sani da Stepanakert.

    Shugabannin yankin sun bayyana a cikin wata sanarwa cewa, ta hanyar shiga tsakani da dakarun wanzar da zaman lafiya na Rasha suka cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta daga karfe ɗaya na rana, agogon yankin.

    • Amurka ta ce a tsagaita wuta a Sudan bayan kashe kusan mutum 200
    • An cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Syria
  2. Yaron da hanjinsa ya ɓace a asibitin Legas ya mutu

    ..

    Asalin hoton, LAGOS STATE GOVERNMENT

    Wani yaro ɗan shekara 12, mai suna Debola Akin-Bright, wanda a baya aka bayar da rahoton ɓacewar ƴan hanjinsa a asibiti, ya rasu.

    Ɗaya daga cikin iyalan yaron ne ya tabbatar wa BBC da hakan, inda ya ce kafin mutuwarsa, yaron ya yi fama da zuban jini a cikin tumbinsa.

    Ya ce iyalin sun garzaya da yaron ne zuwa asibiti, inda aka zarce da shi wurin bayar da kulawa ta musamman na Asibitin Koyarwa na Jami'ar jihar Legas, inda a can ne rai ya yi halinsa.

    Tun farko yaron dai ya shiga matsanancin hali bayan jerin tiyata da aka yi masa a baya, inda a nan ne aka tabbatar da cewa babu wani ɓangare na hanjinsa.

    A tattaunawar da ta yi da BBC, a farkon watan Satumba, mahaifiyar yaron, Mrs Deborah Akin-Bright, ta ce ta kasa gane yadda za a ce hanjin ɗanta ya ɓace kuma ba a san wanda ya ɗauka ba.

    A cikin tattaunawar, ta ce tun farko an kai yaron wani asibiti ne mai zaman kansa bayan ya fara amai tare da gudawa na kwana biyu.

    Sai dai bayan kula da shi na kimanin kwana biyu ba tare da samun sauƙi ba, an yi wa yaron hoton ciki, inda aka gano cewa yana fama da cutar tsakuwar hanji (Appendicitis), da fashewar hanji.

    Inda bayan yin hoto na biyu aka ƙara gano cewa yana kuma fama da toshewar hanji.

    Wannan lamari ne ya sa aka gudanar da tiyata ba tare da ɓata lokaci ba.

    Sai dai bayan yin tiyata har sau biyu a asibitin mai zaman kansa, jikin Debola ya ci gaba da rincaɓewa, inda iyayensa suka lura cewa wani abu na ɗiga a cikin cikinsa, lamarin da ya tursasa wa iyayen ɗaukan shi zuwa Asibitin Koyarwa na Jami'ar jihar Legas.

    A cikin kwanankin farko bayan kai yaron Asibitin koyarwa, lamarin nasa ya ci gaba da dagulewa, inda wurin da aka yi aiki na farko ya fashe, kuma ruwa ya ci gaba da tuɗaɗowa.

    Daga nan ne aka yanke shawarar yi wa yaron wata tiyatar.

    Sai dai bayan buɗe cikinsa likitoci sun shaida wa iyayen cewa ba su ga ƙaramin ƴaƴan hanji na yaron ba, kuma akwai yiwuwar cewa sun ɓace ne a asibitin farko.

    Mrs Debora ta ce "a lokacin da likita ke yi min bayanin ɓacewar ƴaƴan hanjin na kasa fahimtar me yake nufi, na shafe kwanaki ina tunanin cewa ƙarya suke yi, ta yaya za a ce babu hanji a cikin mutum?"

    Ta ƙara da cewa "na sharɓi kuka kamar zan mutu, ta yaya wannan yaro zai rayu babu hanji?"

    Bayan ɓullar labarin ɓacewar hanjin yaron ne gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ya ziyarci yaron, tare da yin alƙawarin ɗaukar nauyin kula da shi.

    Bugu da ƙari ita ma Majalisar Dokokin jihar Legas ta kafa wani kwamiti domin yin bincike kan ɓacewar ƴaƴan hanjin marigayin.

    Likitoci a Asibitin Koyarwa na Jami'ar jihar Legas sun dage kai-da-fata kan bayaninsu na rashin ganin ƴaƴan hanji a cikin yaron, kuma sun ce suna da bidiyon tiyatar da suka yi, wanda ke zaman shaidar cewa babu hanjin a lokacin da suka buɗe cikin marigayi Debola.

    • An yi safarar sa don cire masa ƙoda yanzu kuma ya shiga ɓuya
    • Kotu ta samu Ekweremadu da laifin yunƙurin safarar sassan ɗan adam
  3. Wutar daji ta mamaye yankunan Australia

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Masu kashe gobara a jihar New South Wales ta Australia na ƙokarin kashe wutar daji daban-daban har 70 da ta mamaye yankunan jihar.

    Yanayi na zafi da na iska na barzanar ta'azzara wutar daji da jefa mazauna yankunan da ke kewaye da birnin Sydney a cikin gagarumin hadari.

    Ana fama da tsananin zafi a yankunan kasar da dama.

    Mahukunta a Australia sun tabbatar da cewa mahaukaciyar gugguwa wadda ake kira da El Nino na tunkarosu.

    Al'amarin na sake haifar da barazana da jefa mutane cikin yanayi na damuwa kan ƙaruwar wutar dajin.

    • Wutar daji ta ƙone wani gari ƙurmus a Amurka
    • Wutar daji ta tilasta kwashe mutanen wani gari a Kanada
  4. Burtaniya za ta fitar da sabbin tsare-tsare kan ɗumamar yanayi

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Firaministan Burtaniya Rishi Sunak ya tabbatar da cewa a wannan makon zai fitar da cikakkun bayanai kan tsare-tsaren gwamnatinsa game da ɗumamar yanayi.

    A ranar Talata an shaida wa BBC cewa Sunak na duba yiwuwar sassauta wasu tsare-tsarensa na muhalli, ciki har da jinkirta haramcin sayar da sabbin motocin da ke amfani da man fetur da diesel, da kuma shirinsa na rage amfani da na'urorin da ke fitar da sinadarai masu gurɓata muhalli.

    Firaministan ya dage kan cewa burin gwamnatin ƙasar shi ne kawo karshen fitar da hayaƙi ko sinadarai masu gurbata muhalli kafin shekara ta 2050, amma ta hanyoyi mafi dacewa.

    Sai dai yayin da wasu ke maraba da matakin, wasu na ganin akwai gagarumar matsala.

    • Sauyin yanayi: Me ya sa matsalolinsa ke ƙara ta'azzara a duniya?
    • An yi gargadi ga shugabanni kan dumamar yanayi
  5. Ƙasashe 32 za su nuna goyon bayansu ga Ukraine

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, ...

    Lauyoyin ƙasashe 32 da ke marawa Ukraine na shirin nuna goyon-bayansu kan ƙarar da ƙasar ta kai a kan Rasha a kotun duniya.

    Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya da ke Hague na duba ko tana da hurumin sauraron wannan kara.

    Ukraine ta shigar da wannan ƙara ne a gaban kotu bayan mamayar Rasha a kasarta a bara.

    A wani yanayi na goyon-bayan da ba a taba gani ba, Ƙasashen 32 da suka hada da Burtaniya da Canada da sauran kasahen Turai sun nuna suna tare da Ukraine.

    Ƙasar na cewa Rasha ta take dokar MDD ta kisan kiyashi wajen kai musu hari, a bisa yaudara.

    Rasha dai ta musanta wadannan zarge-zarge. Idan ta bukaci a yi watsi da karar.

    • Yadda ɓarnar da Rasha ta yi a Ukraine ta jefa ƙasar cikin duhu
    • Amurka ta amince Denmark da Netherland su bai wa Ukraine jiragen yaƙi
  6. An fara karanta hukuncin zaɓen gwamnan Kano ta manhajar 'Zoom'

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Alƙalai sun fara karanto hukuncin kotun sauraron ƙarfin zaɓen gwamnan Kano na 2023, sai dai ana karanto hukuncin ne ta manhajar zoom.

    Ma'ana alƙalan kotun ba su samu halartar harabar kotun da kansu ba.

    Sai dai lauyoyi da wakilan jam'iyyun da lamarin ya shafa suna zaune a cikin kotun inda suke kallo da sauraron hukuncin ta majigi.

    Ya zuwa yanzu dai babu masaniya kan dalilan da suka sanya alƙalan suka gaza halartar zaman da kansu a harabar kotun da ke cikin birnin Kano.

    Sai dai kafin ranar yanke hukuncin al'amuran siyasa sun yi zafi tsakanin magoya bayan manyan jam'iyyu biyu, APC da NNPP, da ke hamayya da juna a jihar.

    Kuma a baya babbar alƙaliyar kotun ta koka kan yadda wasu ke yunƙurin bai wa kotun cin hanci domin samun nasara.

    • Zaɓen Najeriya 2023: Sakamakon zaɓen gwamnan jihar Kano
    • Ba mu yarda da sakamakon zaɓen Kano ba – APC
  7. Ƴan sanda sun kafa shinge kan hanyoyin zuwa kotun korafe-korafen zaɓen Kano

    ...

    Jami'an tsaro sun kafa shingaye a hanyoyin da suka haɗa zuwa harabar kotun sauraron ƙarafin zaɓen gwamnan na jihar Kano, gabanin yanke hukunci a yau Laraba.

    A yau ne dai kotu za ta yanke hukunci kan ƙorafin bayan ƙarar da jam'iyyar APC ta shigar domin ƙalubalantar nasarar gwamna Abba Yusuf na jam'iyyar (NNPP) a zaben da aka gudanar a ranar 18 ga watan Mayun 2023.

    An zabi wasu ƴan jarida ƙalilan inda aka hana da dama zuwa kusa da wurin.

    ...
    ...

    Kwamishinan ƴan sandan Najeriya a jihar Kano ya isa harabar kotun domin lura da yadda abubuwa ke gudana.

    ...
  8. An bayar da belin masu yunƙurin auren jinsi ɗaya a Najeriya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, ...

    Wata kotu a Najeriya ta bayar da belin wasu mutane 69 da aka kama a yunƙurin su na gudanar da auren jinsi ɗaya a watan Agusta bayan wani samame da jami'an tsaro suka kai.

    Kamar a yawancin kasashen Afirka ana kallon luwadi a matsayin laifi da rashin ɗa'a a Najeriya.

    Ƙasar dai na da tsauraran dokoki na hana auren jinsi ɗaya.

    Lauyan da ke kare mutanen ya ce za a bayar da belin su amma sai ya miƙa wa kotu kuɗi kwatankwacin dalar Amurka 600 a kan kowanne ɗaya daga cikin mutanen da aka tsare.

    Ƙungiyar kare hakkin bil’adama ta Human Rights Watch ta soki ‘yan sandan Najeriya kan yadda suka gabatar da waɗanda ake zargin a gaban ‘yan jarida a bainar jama’a tare da yi musu tambayoyi kan zargin da ake musu.

    Duk da Allah wadai da kasashen duniya suka yi, an kafa dokar a ƙasa da shekaru 10 da suka gabata da ta haramta auren jinsi ɗaya a bainar jama'a tare da hukuncin daurin shekaru 10 da kuma shekaru 14 ga duk wanda aka samu da laifin yin auren jinsi.

    A shekarar 2019 ‘yan sanda a jihar Legas sun gurfanar da wasu mutum 47 a gaban ƙuliya amma kotu ta yi watsi da ƙarar saboda ‘yan sanda sun kasa bayyana da kuma gabatar da shaidu.

    • An yanke wa 'yan luwadi hukuncin kisa a Bauchi
    • Manyan malaman addinai sun yi kira a haramta sauya ‘yan luwadi da madigo
  9. Assalamu alaikum

    Masu bin mu a wannan shafi barkan mu da safiyar Laraba.

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Kuna kuma iya tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa a shafukanmu na sada zumunta.