Kwalara ta kashe mutum 9 a Habasha

Asalin hoton, Getty Images
Hukumomin lafiya a Habasha sun ce mutum 9 sun mutu sakamakon ɓarkewar cutar amai da gudawa a yankin Benishangul-Gumuz da ke arewa maso yammacin ƙasar kamar yadda tashar talabijin na ETV ya ruwaito a ranar Lahadin da ta gabata,
Wani jami'in kiwon lafiya na yankin, Abdulmunhem Al-Beshir, ya ce "wasu mutum 131 ne suka kamu da cutar yayin da kuma wasu 9 suka mutu," in ji ETV.
An samu bullar cutar a gundumomi uku, a cewar hukumar lafiya ta Benishangul-Gumuz.
A halin da ake ciki kuma, barkewar cutar kwalaran ta kuma kashe 'yan gudun hijirar Sudan 9 a yankin Amhara da ke arewa maso yammacin Habasha.
Kafofin yaɗa labaran cikin gida sun ce annobar kwalara ta bazu a yankuna 11 na kasar a cikin shekarar da ta gabata, inda ta kashe mutum 320.
Yaƙin basasa na shekaru biyu da fari ya haifar da mummunan rikicin jin kai a yankin






