Aljeriya ta gabatar da tsarin sasanta rikicin siyasar Nijar

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

A'isha Babangida and Umar Mikail

  1. Al-Shabab ta kwace yankuna daga hannun sojojin Somalia

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, ...

    Mayakan kungiyar al-Shabab sun sake kwato akalla wurare biyu da sojojin Somaliya suka kwace a wani sabon farmaki da suka kai.

    Akwai rahotannin da ke cewa bangarorin biyu sun samu gagarumar asara a lokacin da ake gwabza kazamin fadan neman iko da Cowsweyne.

    Majiyoyi a wani asibitin sojoji sun ce an kai akalla sojoji 50 da suka jikkata domin samun kulawa.

    Shugaba Hassan Sheikh Mohamud dai ya yi alkawarin kawo ƙarshen al-Shabab cikin watanni.

    A ranar Juma'ar da ta gabata sojoji da mayakan sa-kai sun yi shagulgulan murnar karbe wani sansanin mayakan al-Shabab da ke El Bur.

    • Masu mayafi da ke yaƙar mayaƙan al-Qaeda da al-Shabab a Somaliya
    • Al-Shabab ta ce ta kame wani otal a Somalia
  2. Assalamu alaikum

    Masu bin mu a wannan shafi barkanmu da warhaka.

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a wannan safiya ta Talata domin kawo muku halin da duniya ke ciki, musamman Najeriya da makwabtan kasashe.

    Kuna kuma iya tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa a shafukanmu na sada zumunta.

    Mu je zuwa....