Gwamnatin Najeriya ta bayyana wuraren da za a iya samun ambaliya a bana

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

A'isha Babangida, Mukhtar Adamu Bawa, Ibrahim Yusuf Mohammed and Haruna Kakangi

  1. An bai wa ƙasashen Afirka 12 rigakafin Maleriya

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    An ware allurai miliyan 18 na rigakafin cutar zazzabin cizon sauro na farko (RTS,S) ga kasashen Afirka 12 na tsawon shekaru biyu masu zuwa.

    Akalla kasashen Afirka 28 ne suka nuna sha'awar karbar allurar rigakafin cutar maleriyar, amma kasashe 14 ne kawai suka mika buƙata ga ƙungiyar GAVI, kungiyar da ke kula da shirin rigakafin.

    Ghana da Malawi da kuma Kenya ne za su kasance kasashe na farko da za su karbi allurar a cikin watannin karshen wannan shekaran. Maleriya na daya daga cikin cututtukan da suka fi kashe mutane a Afirka.

    Kusan kowane minti daya, a nahiyar, yaro dan kasa da shekaru 5 na mutuwa sakamakon kamuwa da cutar zazzabin cizon sauro.

    Buƙtar da aka riga aka yi kan allura miliyan18 din da aka ware na maganin RTS, S yana da yawa sosai kuma ya fi ƙarfin abin da ake da shi a ƙasa.

    Hukumar lafiya ta duniya (WHO), da ƙungiyar Gavi da sauran abokan hulda sun ce sun yi la'akari da kasashen da suka fi bukata.

    Malawi, Ghana da Kenya wadanda tuni suka yi amfani da allurar rigakafin a wani mataki na gwaji ga akalla yara miliyan 1.7, an ware musu allurai miliyan 6.9.

    A karon farko, kasashe 8 da suka hada da Benin da Burkina Faso da Burundi da Kamaru, da Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo da Laberiya da Saliyo da Uganda, za su kaddamar da rigakafin a cikin shirye-shiryensu na yau da kullun.

    Nijar za ta samu wani bangare na abin da aka yi kasafi. Amma, ƙasashen Mozambik da Sudan ba za su karɓi allurai ba, saboda yawan ficewa da suke yi daga shirye-shiryen rigakafi makamantan wannan.

  2. Gwamnatin Netherlands za ta haramta wa ɗalibai shiga aji da waya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin ƙasar Holland ta sanar da dakatar da amfani na'urori da suka hada da wayoyin hannu a azuzuwa domin hana su kawo cikas wurin karatu..

    An bullo da wannan shirin ne tare da hadin gwiwar makarantu kuma zai fara aiki a farkon shekara mai zuwa.

    Akwai wadansu lokutan da dokar ba za ta yi aiki ba, musamman idan ya shafi ɗalibai masu buƙatar bayanan likitoci a kai a kai ko kuma masu bukatu na musamman, da kuma azuzuwan koyar da aiki da na'urori.

    Wannan haramcin ba doka ba ce amma yana iya zama haka nan gaba.

    "Duk da cewa wayoyin hannu na da matukar muhimmanci a rayuwarmu, amma ba su da wuri a cikin azuzuwa," in ji Ministan Ilimi Robbert Dijkgraaf.

    "Dole ne dalibai su mayar da hankali kuma a ba su duk wata dama don yin karatu da kyau. Mun san daga binciken kimiyya cewa wayar hannu na kawo cikas ga samuwar hakan."

  3. Gwamnan Kano ya ɗibar wa kwamishinoninsa wa'adin wata shida

    Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf

    Asalin hoton, Abba Kabir

    Bayanan hoto, Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf

    Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya tabbatar wa kwamishinonsa cewa za a tantance su bayan wata shida da kama aiki domin sanin waɗanda za su ci gaba da aiki da kuma waɗanda za a kora.

    Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da majalisar zartarwar jihar ta yi zamanta na farko a yau Laraba.

    A cikin jawabin da ya gabatar, Abba ya ce "Ina tunatar da ku cewa kuna da wata shida na gwaji bayan naɗa ku kan muƙami, bayan haka ne za a duba ayyukan da kowace ma'aikata ta gudanar, za a yaba wa waɗanda suka yi ƙoƙari sannan za a yi waje da waɗanda ba su yi ƙoƙari ba."

    • Abu huɗu da Muhuyi zai binciki gwamnatin Ganduje a kai
    • Masu sayen kayanmu sun janye daga Kano saboda rusau - Ƴan kasuwa
  4. Yaro ɗaya na mutuwa cikin kowane daƙiƙa goma - Bincike

    ...

    Yara da matasa miliyan uku ne ke mutuwa a kowace shekara sakamakon cututtuka masu yaduwa, kwatankwacin mutuwar mutum daya a cikin duk dakika 10

    Ƙasashen Indiya, Najeriya da Pakistan ne ke da mafi yawan mutane masu fama da irin wadannan cututtukan, a cewar wani sabon bincike da aka buga a mujallar Lancet.

    An gano cewa cututtuka masu yaduwa sun haddasa fiye da rabin irin wadannan mace-mace a kasashe masu karami zuwa matsakacin karfi, idan aka kwatanta da kashi 6 cikin 100 na kasashe masu karfin tattalin arziki, binciken da Cibiyar Nazarin Yara ta Murdoch da ke Australia, da Cibiyar kididdigar alkaluman kiwon lafiya ta Amurka ta ce.

    Binciken da aka yi a cikin kasashe 204 daga tsakanin shekarun 1990 zuwa 2019, ga mutane daga lokacin haihuwa zuwa shekaru 24, ya gano matakan hana kamuwa da cuta sun fi mayar da hankali kan yara 'yan kasa da shekaru biyar, tare da karancin kulawa ga matasa tsakanin shekaru biyar zuwa 24.

    Bayan la'akari da wadannan sauye-sauyen alƙaluman nauyin cututtukan, binciken ya yi kira da duk yunkurin da ake yi na magance cututtuka a duniya su mayar da hankali kan yaran da suka tasa da kuma matasa.

    Cututtuka kamar gudawa, da ciwon huhu da zazzabin cizon sauro sun kai kashi biyu bisa uku na cututtuka masu yaduwa da ke haddasa mutuwa a cikin wannan adadi, yayin da cuta mai kashe garkuwan jiki da tarin fuka aka gano su ne kan gaba cikin cututtukan da ke addaban matasa.

    • Yadda jarirai suka mutu a asibiti sanadiyyar yanke wutar lantarki
    • Yadda girman halittar 'mamana' ke hana ni sakewa
  5. Isra'ila na iƙirarin nasara a Jenin, ko matakin da ta ɗauka zai magance matsalar?

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Wani sojan Isra'ila a kan motan buludoza masu sulke kusa da shingen bincike na Jalamah a ranar 4 ga Yuli

    Akwai hare-haren jiragen sama marasa matuki, da motoci masu sulke da kuma daruruwan sojoji da ke da hannu a babban farmakin soji na Isra'ila na kwanaki biyu a sansanin 'yan gudun hijira na Jenin, wanda ba a ga irin shi ba tsawon shekaru da dama.

    Rundunar ta ce ta gano ɗakunan ajiya da gwaje-gwajen makamai, wanda kuma a yau ta ke nuna wa ‘yan jarida dimbin bindigogi, harsasai, bama-bamai da rigunan kariya da ta ce ta kama a sansanin.

    Ta ce an same su ne wuraren ɓuya na musamman, da masallaci, da ramuka da kuma a cikin motoci.

    ...
    Bayanan hoto, ...

    Rundunar sojin Isra'ila ta yi ikirarin cewa dukkanin Falasɗinawa goma sha biyu da matasa maza da suka mutu a farmakin da suka kai 'yan ta'adda ne kuma ta yi nasarar kauce wa asarar rayukan fararen hula da ba su ɗauki makamai ba.

    Zuwa yanzu dai, an tabbatar wa BBC cewa takwas daga cikin waɗanda suka mutu suna bangaren sojan manyan ƙungiyoyin Falasɗinu ne.

    Wani Likitan Falasdinu ya sake shaida wa BBC cewa fararen hula na cikin mutane 120 da suka jikkata.

    Masu nazari kan ayyukan sojojin Isra'ila na tsawon lokaci sun yi nuni da cewa tasirin wannan farmakin taƙaitacce ne.

    "Farmakin Isra'ila shure-shure ne, wanda ba ya hana mutuwa," in ji Avi Issacharoff, wani fitaccen ɗan jarida.

    Ya yi hasashen cewa "sansanin 'yan gudun hijira na Jenin zai rage zama wuri mai hatsari."

    • Ina ne sansanin Jenin, kuma me ya sa rikici ke ta'azzara a yankin?
    • Dakarun Isra'ila sun kai hari cikin Masallacin Kudus
  6. Roberto Firmino ya koma Al-Ahli ta Saudiyya

  7. Ana kai wa baƙi hari a Tunisiya, ana 'jefo wasu daga saman bene'

    ...

    Asalin hoton, AFP

    An kai hari kan wasu baƙin haure daga yankin kudu da hamadar sahara a birnin Sfax na ƙasar Tunisiya, tare da jikkata wasu da dama.

    Rikicin dai ya samo asali ne sakamakon kisan da aka yi wa wani dan ƙasar Tunusiya a ranar Litinin, yayin da wata hatsaniya da ƴan ci-rani.

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Wata ƙungiya mai zaman kanta ta ce a hare-haren ramuwar gayya, an jefo wasu ƴan ci-rani daga saman baranda, wasu kuma an kai musu hari da takubba.

    Mata da yara na daga cikin waɗanda aka kai wa harin.

    Shaidu sun ce an tilasta wa mutane da dama ficewa daga birnin, wanda ke zama muhimmin wurin fara tafiya ga masu neman tsallakawa ƙasashen Turai ta hanyar jirgin ruwa zuwa tsibirin Lampedusa na Italiya.

  8. NCDC ta bayyana mutanen da suka fi haɗarin kamuwa da cutar mashaƙo ta Diphtheria

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa ta Najeriya, NCDC ta bayyana jerin wasu mutane da ta ce su ne suka fi shiga haɗarin kamuwa da cutar mashaƙo ta diphtheria.

    Diphtheria dai wata cuta ce ta mashaƙo wadda ke shafar hanci da maƙoshi, da kuma fatar jikin mutum a wasu lokuttan.

    A cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na twitter, ranar Laraba, NCDC ta ce mutanen da ke cikin haɗarin kamuwa da cutar mashaƙo ta diphtheria sun haɗa da:

    • Yara da manya waɗanda ba su taba karɓar rigakafin cutar diphtheria ba.
    • Ma'aikatan kiwon lafiya da sauran waɗanda suka yi cudanya da wadanda ake zargin sun kamu da cutar.
    • Mutanen da ke zaune a cikin cunkoson jama'a da kuma mutanen da ke zaune a wuraren da ba su da tsafta.
  9. Majalisar wakilai ta dakatar da JAMB daga hukunta yarinyar da 'ta ƙara wa kanta maki'

    ...

    Asalin hoton, JAMB

    Majalisar wakilai ta Najeriya ta tsoma baki cikin batun zargin da hukumar shirya jarabawar shiga jami’a (JAMB) ta yi wa wata daliba mai suna Mmesoma Ejikeme na kirkirar sakamakon jarabawa na bogi wanda hukumar ta shirya na shekarar 2023.

    ‘Yan majalisar sun nuna damuwarsu kan yadda hukumar jarabawar ta gaza nuna dattaku kan lamarin da ya shafi karamar yarinya ta hanyar janye sakamakon jarabawarta tare da dakatar da ita na tsawon shekaru uku.

    Sun ce yana yiwuwa akwai hannun wani a cikin lamarin.

    Daga nan ne majalisar ta kafa kwamitin da zai binciki lamarin tare da neman hukumar JAMB da ta dakatar da zartar da hukunci har sai majalisar ta kammala bincikenta.

    A ranar Lahadin da ta gabata ne hukumar ta JAMB ta zargi dalibar da kirkirar sakamakon bogi a jarabawar ta bana.

  10. Wasu na ƙorafi, NNPP na dariya da shugabancin Majalisar Najeriya

  11. Gwamnati ta bayyana yankunan da za a iya samun ambaliyar ruwa a Najeriya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Tarayya ta fitar da sanarwar hasashen ambaliya a shekara ta 2023, inda ta ce jihohi 14 da al’ummomi 31 za su iya ganin ruwan sama kamar da bakin kwarya da zai iya haifar da ambaliya daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Yuli.

    Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da ma’aikatar kula da muhalli ta tarayya ta fitar.

    A cewar sanarwar, an gano jihohin da al’ummomin da suka hada da:

    Plateau - Langtang, Shendam

    Kano - Sumaila, Tudun Wada

    Sokoto - Shagari, Goronyo da Silame

    Delta - Okwe

    Kaduna - Kachia

    Akwa Ibom - Upenekang

    Adamawa - Mubi, Demsa, Song, Mayo-Belwa, Jimeta, Yola

    Katsina - Katsina, Jibia, Kaita da Bindawa

    Kebbi - Wara, Yelwa da Gwandu

    Zamfara - Shinkafi, Gummi

    Borno - Briyel

    Jigawa - Gwaram

    Kwara - Jebba

    Niger - Mashegu, Kontagora

    Gwamnatin ta kuma bukaci masu ruwa da tsaki a jihohin da abin ya shafa da su dauki matakan kariya domin kiyaye asarar rayuka da dukiyoyi.

    • Mahaifiyar da ta rasa 'ya'ya uku a jirgin da ya nutse da 'yan biki a Kwara
    • Yadda ake wahalar ruwa a sassan birnin Kano
    ...
  12. An yanke wa Indiyawan da suka kashe wani Musulmi ɗaurin shekara goma

    ...

    Asalin hoton, BBC HINDI

    Bayanan hoto, Wani faifan bidiyo ya nuna Ansari yana rokon mutane da ke dukansa da su bar shi da ransa ya yaɗu a shafukan sada zumunta

    Wata kotu a Indiya ta yanke wa wasu maza 10 hukuncin daurin shekaru 10 a gidan yari saboda samun su da laifin dukan wani musulmi har ya mutu, shekaru hudu da suka gabata.

    Tabrez Ansari, mai shekaru 24 ya mutu ne kwanaki kaɗan bayan harin da wasu mutane suka kai masa bayan sun zarge shi da satar babur a jihar Jharkhand da ke gabashin ƙasar.

    Wani faifan bidiyo da aka riƙa yaɗawa, ya nuna yadda aka tilasta wa marigayin ya yi kalaman yabo ga abin bauta na addinin Hindu, yayin da yake magiya tare da roƙon kada a kashe shi.

    Lamarin ya haifar da cece-ku-ce tsakanin al'umma.

    Iyalin matashin sun zargi ƴan sanda da hana su ganin ɗan nasu.

    Sai dai rundunar ‘yan sandan jihar ta musanta hakan.

    Bidiyon da aka riƙa yaɗawa da aka ɗauka a daren 19 ga watan Yunin 2019 ya nuna Ansari cikin halin ban tausayi, kuma daure a jikin sandar wutan lantarki cikin taron mutane, yayin da jini da hawaye ke gudana a fuskarsa.

    Maharan nasa sun tilasta masa faɗin "Jai Shri Ram", ma'ana "nasara ga ubangiji Ram".

    Ansari ya yi yadda suka ce, amma mutanen suka ci gaba da farmasa. Washe-gari aka miƙa shi ga ƴan sanda, wadanda suka tuhume shi da laifin sata.

  13. Carlo Ancelotti zai zama kocin Brazil a 2024

  14. Majalisar wakilai za ta binciki asusun TETFUND kan zargin almundahana

    ...

    Asalin hoton, OTHER

    Bayanan hoto, ...

    Majalisar Wakilai ta ce za ta binciki zargin almundahana da kuɗi naira Tiriliyan 2.3 a Asusun tallafa wa manyan makarantu (TETFUND) daga shekarar 2011 zuwa 2013.

    An cimma wannan matsaya ce bayan amincewa da wata buƙata da wasu ƴan majalisa: Olusola Fatoba, David Fouh da Zakari Nyanpa suka gabatar.

    A lokacin gabatar da buƙatar, Fatoba, ya ce tun da aka kafa Asusun Tallafawa Manyan Makarantu a shekarar 2011, asusun ya samu maƙudan tiriliyoyin naira a matsayin kudaden shiga.

    Jaridar punch ta ruwaito cewa Fatoba ya yi zargin cewa "akwai zargin badaƙala a wajen gudanar da ayyukan asusun, musamman a wajen bayar da kwangila da kuma aiwatar da ayyuka."

    “Tsarin aiki a cikin asusun Tallafa wa Manyan Makarantu yana da yawa kuma hakan na iya haifar da rashin sa ido a kan ayyukan da ake yi, tare da raba kuɗaɗen ba tare da bin diddigin abun da aka yi da su ba, da biyan kuɗi ma ƴan kwangila duk da gazawar su ta cimma nasarorin da ake buƙata da kudin."

    Dan majalisar ya ce idan ba a dauki matakan gaggawa ba don bincikar wannan zargin, "lalacewar tsarin makarantu" za ta ci gaba da karuwa.

    Majalisar ta kafa wani kwamiti na wucin-gadi da zai binciki zarge-zargen tare da bayar da rahoto cikin makonni hudu domin ci gaba da daukar matakin shari’a.

  15. 'Na zaɓi komawa Manchester bayan Erik ten Hag ya faɗa min shirinsa'

  16. Hotuna: Rayuwa bayan babban farmakin da Isra'ila ta kai Jenin

    Kwana biyu bayan babban farmakin da sojojin Isra'ila suka kai a Jenin, ana iya ganin ɓarnar da aka yi a yankin jim kaɗan da ficewar sojojin Isra'ila.

    Kamar yadda ake iya gani a cikin waɗannan hotuna, ba ƙaramin barna aka tafka ba a cikin birnin.

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, Mutane suna wucewa ta kan tarkace da ɓaraguzai don kai abinci - wanda ƙungiyoyin ba da agaji suka kai
    ...

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, Ga lalatattun motoci a wani titi na birnin Jenin
    ...

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, An ruguza gidaje a sansanin 'yan gudun hijirar na Jenin
    ...

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, An lalata gine-gine da dama a yayin farmakin
  17. Sojojin Somaliya sun maye gurbin dakarun AU da suka fice

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, ...

    Dakarun Somaliya sun karɓi ragamar al'amuran tsaro a yankuna biyar cikin shida da sojojin Tarayyar Afirka suka kasance a ƙasar.

    Ma'aikatar tsaron Somaliya ta ce ta yaba da irin sadaukarwar da rundunar Tarayyar Afrika suka yi a tsawon shekaru, da kuma ƙasashen da suka bayar da gudunmawar sojojin.

    Sanarwar ta zo ne bayan shirin janye sojojin Tarayyar Afirka 2,000 - waɗanda ake sa ran za su fara ficewa tun daga ranar 30 ga watan Yuni.

    Galibin sansanonin sojin da aka mika wa dakarun Somaliya zuwa yanzu suna cikin yankin Lower Shabelle kuma sojojin Burundi ne ke gudanar da ayyuka.

    Ana sa ran ƙarin sojojin Tarayyar Afirka 3,000 za su fice a karshen watan Satumba - kafin ficewar ɗaukacin sojojin tabbatar da zaman lafiya a Somaliya karshen shekarar 2024.

    AU dai tana taimakawa gwamnatin Somaliya a yaƙin da take yi da kungiyar ƴan ta-da-ƙayar-baya ta al-Shabab tun daga 2007.

  18. Ana bincike don gano yadda hodar iblis ta shiga fadar White House

  19. An yi babban taron jana'izar Falasɗinawan da aka kashe a Jenin

    Jama'a sun cika titunan Jenin a safiyar yau domin jana'izar Falasɗinawan da aka kashe a babban farmakin da sojojin Isra'ila suka kai a sansanin.

    An kashe Falasɗinawa 12 da sojan Isra'ila daya tun ranar Litinin.

    Falasɗinawa

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Mutanen da suka hallara sun riƙa ɗaga tutocin Falasdinu
    Falasɗinawa

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, An kai gawawwakin waɗanda aka kashe masallaci domin yi musu sallah
    Falasɗinawa

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Ana iya ganin babban taron jana'izar a wannan hoton
  20. An zabga rana mafi tsananin zafi a tarihi

    ...

    Asalin hoton, STR

    Bayanan hoto, ..

    Yanayin zafi a duniya ya kai wani sabon matsayi a ranar Litinin 3 ga watan Yuli, inda ya cimma maki 17 a ma'aunin salsiyas wanda hakan ke nuna rana mafi zafi a karon farko.

    Wannan ya karya tarihin bayan na maki 16.92 a ma'aunin salsiyas da aka samu a watan Agusta 2016.

    Masanan kimiyya sun ce nazarin da aka yi shi ne ƙurewar maki a duk wani ma'auni da aka taɓa amfani da shi tun a ƙarshen ƙarni na 19.

    Tsananin zafin ya faru ne sakamakon haɗakar yanayin ɗumamar ruwan sararin ƙasa da ake kira El Nino da fitar da gurɓatacciyar iskar kabon da ake ci gaba da samu.

    Masu bincike sun yi imanin cewa za a samu ƙarin bayanai a cikin watanni masu zuwa yayin da yanayin El Niño ke ƙara ƙarfi.

    Tun farkon wannan shekara, masu bincike suna ƙara nuna damuwa game da ƙaruwar yanayin zafi a ƙasan teku.