'Yan bindiga sun kashe ɗan jarida a arewacin Kamaru
An harbe wani ɗan jarida a yankin arewa maso yammacin Kamaru da ke fama da rikice-rikice.
Wannan shi ne karo na uku da ake kashe ɗan jarida a wannan shekara a ƙasar.
Rahotonni sun ce an harbe Anye Nde Nsoh a wata mashaya a birnin Bamenda a lokacin da wasu mahara da ba a san ko su wane ne ba suka buɗe wuta.
Birnin Bamenda na ɗaya daga cikin wuraren da tashe-tashen hankula masu alaƙa da hare-haren 'yan awaren ƙasar masu magana da Turancin Ingilishi.
Sauran 'yan jarida biyun da aka kashe a ƙasar cikin wannan shekara, an kashe su ne a birnin Yaoundé.


