BVAS na bayar da matsala a wasu sassan Maiduguri

Asalin hoton, INEC
Yayin da harkokin zaɓe ke ci gaba da gudana a wasu sassan Najeriya lami lafiya, wasu ɓangarorin suna fama da matsaloli da dama.
Kama daga rashin isar jami'an INEC a kan lokaci zuwa na rashin tsaro kamar a abin da ya faru a jihar Gombe.
Sai dai matsalar da ake fsukanta a Maiduguri babban birnin Jihar Borno ta sha ban-ban da ta sauran jihohi.
A Maidugurin matsalar na'urarar tantance masu kaɗa ƙuri'a ita ce ta ƙi aiki yadda ya kamata.
Kazalika ana fuskantar rashin fitowar masu zaɓe kamar yadda mai turo wa BBC bayani daga Maiduguri, Adamu Aliyu Ngulde ya tabbatar wa BBC.










































