An kunna fitilu domin ci gaba da zaɓe a wasu sasssan Najeriya

Wannan shafi zai rinƙa kawo uku abubuwan da ke faruwa game da zaɓen shugaban ƙasa da na majalisar dokokin tarayya a Najeriya.

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Buhari Muhammad Fagge, Yusuf Yakasai, Abdullahi Bello Diginza and Nabeela Mukhtar Uba

  1. Ƙungiyar Commonwealth ta yaba da yadda zaɓen Najeriya ke tafiya

    Zaɓen Najeriya

    Asalin hoton, Commonwealth/Twitter

    Shugaban kungiyar sa ido kan zaɓen Najeriya ta Commonwealth, Thabo Mbaki ya buƙaci dukkan masu zaɓe da su fito su zaɓi waɗanda suke so domin shugabantar su.

    Thabo Mbeki wanda ya kasance tsohon shugaban ƙasar Afirka ta Kudu, ya bayyana haka ne lokacin da masu sa ido na kungiyar suka ziyarci wasu rumfunan zaɓe a Abuja babban birnin Najeriya.

    Kungiyar ta ƙasashe renon Ingila na sa ido ne a daidai lokacin da miliyoyin 'yan Najeriya suka fita rumfunan zaɓe daban-daban da ke faɗin ƙasar domin zaɓan shugaban ƙasa da kuma 'yan majalisar dattawa da kuma wakilai.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  2. Ana ci gaba da ƙirga ƙuri'u a wasu sassan Legas

    BBC
    BBC
    BBC
    BBC
  3. An fara ƙirga ƙuri'un zaɓe a Abuja da Bauchi da Legas

    Bayanan bidiyo, Latsa nan domin kallon yadda aka fara ƙirga ƙuri'un
  4. Tsohon shugaban Najeriya Abdussalami ya kaɗa ƙuri'arsa

    BBC
    BBC
    BBC
    BBC
  5. Yadda kasuwa ta buɗewa wasu a rumfunan zaɓe a Kano

    Yayin da ake ci gaba da kaɗa kuri'a, a gefe guda kuma masu sayar da abinci da nama da sauran kayan abinci kasuwa ce ta buɗe musu a mazaɓar Kwankwaso a ƙaramar hukumar Madobi da ke jihar Kano.

    Zaɓen Najeriya
    Zaɓen Najeriya
    Zaɓen Najeriya
    Zaɓen Najeriya
  6. Muna ci gaba da kawo muku yadda zaɓen Najeriya na 2023 ke tafiya

    Ga waɗanda suka shigo shafin a yanzu, bari mu sake tuna muku abubuwan da suka faru kawo yanzu da ya kasance ranar da miliyoyin 'yan Najeriya suka fita rumfunan zaɓe domin zaɓen shugaban ƙasa da kuma 'yan majalisar tarayya.

    • 'Yan Najeriya sama da miliyan 87 suka yi rajista domin ƙada zaɓe. Yawancin waɗannan masu zaɓe matasa ne, inda kuma su suka fara fita rumfunan zaɓe tun sanyin safiya domin kaɗa kuri'arsu.
    • A wasu wurare an samu jinkirin fitowar malaman zaɓe da kuma matsalar na'urar tantance masu kaɗa kuri'a ta BVAS.
    • Tuni aka fara ƙirga ƙuri'a a wasu sassan Najeriya, kamar Abuja da Legas, da Bauchi.
    • A jihar Legas masu zaɓe ne suka fusata saboda rashin kai musu kayan zaɓen.
    • A can jihar Gombe kuwa, wasu ne da ake zargin ƴan bangar siyasa suka far wa jam’ian zaɓe na wucin-gadi da aka tura wata rumfar zaɓe da ke cikin garin Gombe.
    • Dukkan manyan takarar kujerar shugaban ƙasa na Najeriya sun samu damar kada kuri'arsu kama daga Bola Tinubu na jam'iyyar APC da Atiku Abubakar na PDP da Rabiu Kwankwaso na NNPP da kuma Peter Obi na jam'iyyar Labour.
  7. An fara kirga kuri'u a Abuja da wasu sassan Najeriya

    Zaɓen Najeriya

    Bayan kammala kaɗa kuri'a a rumfar zaɓe ta Gana street da ke uunguwar Maitaiama a Abuja, babban birnin Najeriya, tuni aka fara kirga kuri'u.

    Wakilkin BBC Ibrahim Isa wanda ya halarci wajen, ya ce an fara ƙirgen ne da misalin karfe 2:30 na rana.

    A garin Bauchi ma, bayanai na cewa an fara ƙirga ƙuria a garin Ningi da wasu sassan.

    A birnin Legas ma tuni aka fara ƙirga ƙuri'a a unguwar Surelere.

    Zaɓen Najeriya
  8. Shugaban jam'iyyar PDP na Abuja ya rasu

    PDP

    Asalin hoton, PDP

    Shugaban jam'iyyar PDP na babban birnin tarayya Abuja ya rasu a wani haɗarin mota.

    Sunday Zakka wanda yake cikin motarsa Peugeot ƙirar 406 ya yi haɗarin ne tare da mai gadinsa da matuƙinsa, kuma rahotanni na cewa nan mutum biyu suka mutu a cikin motar.

    Haɗarin ya faruy ne da misalin ƙarfe 3:30 na dare lokacin da yake kan haryarsa ta koma gidansa da ke Kuje daga cikin garin Abuja.

    An garzaya da shi asibitin koyarwa da ke Gwagwalada amma daga baya aka mayar da shi babban asibiti na ƙasa da ke cikin garin Abuja, inda kuma a nan ne rai ya yi halinsa.

    Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar PDP Atiku Abubakar ya aike da saƙon ta'aziyya kan mutuwar shugaban na PDPn Abuja.

  9. Muna sane da ƙalubalen da ake fuskanta a wasu yankuna - INEC

  10. EFCC ta kama mutum uku a Kaduna da Kano da Abuja bisa zargin sayen kuri'a

    EFCC

    Asalin hoton, EFCC/FACEBOOK

    Hukumar yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya (EFCC), ta kama wata mata da katunan zaɓe 18 a jihar Kaduna da kuma wasu a Kano da Abuja.

    Jami’an hukumar ne suka kama matar da safiyar yau a unguwar Badarwa da ke Kaduna bayan kai wani samame.

    An kuma samu wata takarda ɗauke da jerin sunayen masu zaɓe guda 17 da asusun ajiyarsu na banki da lambobinsu na waya a matsayin waɗanda ke da damar yin zaɓe a mazaɓar Badarwa/Malali 01 da 08 da ke karamar hukumar Kaduna ta Arewa.

    An kama ta ne lokacin da jami’an na EFCC suka bad-da-kama, inda suka nuna cewa za su sayar da katunansu na zaɓe.

    A halin yanzu dai tana hannun jami’an na EFCC a shiyyar Kaduna, inda suke ƙoƙarin gano wasu mutane da ke tare da ita waɗanda ta ce su ma suna karɓar katunan zaɓen mutane da kuma ba su kuɗi ta amfani da POS da kuma tura kuɗin ta intanet.

    EFCC

    Asalin hoton, EFCC/FACEBOOK

    A Kano kuma EFCCn ta ce ta kama wani mutum da take zargi da sayen kuri’u, inda suka same shi da tsabar kuɗi naira 194,000 a rumfar zaɓen Gidan Zakka da ke Goron Dutse a karamar hukumar ƙwaryar birnin Kano.

    EFCC

    Asalin hoton, EFCC/FACEBOOK

    A Abuja kuma hukumar ta ce ta yi nasarar kama wakilin wata jam’iyya yana sayen kuri’u a karamar hukumar Abaji na babban birnin tarayya, ta hanyar tura musu kuɗi ta intanet.

  11. Wike ya samu damar kaɗa kuri'arsa

    Wike

    Gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike ya samu damar kaɗa kuri'arsa bayan da ya gamu da matsala da na'urar BVAS lokacin da ya zo zabe da safe.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  12. 'Yan banga sun tashi zaɓe a jihar Kogi

    BBC

    Rikicin zaɓe ya ɓarke a yankin Anyigba da ke ƙaramar hukumar Dekina a jihar Kogi.

    Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an kashe wani matashi da ake kira Akayama a yayin rikicin.

    Wasu ‘yan daba ne da suka kutsa kai wajen zaɓen suka kashe mutumin tare da lalata kayan zaɓen.

    Da misalin ƙarfe 11 na safiyar Asabar lamarin ya faru. Tuni dai ƴan bangar siyasar suka karɓe iko da garin suna ta lalata kayan zaɓe a yankuna daban-daban.

    Rahotanni na cewa mamacin ya gama jami’a inda ya karanta bangaren tattalin arziki a jami’ar Prince Abubakar Audu, an kuma harbe shi ne a rumfar zaɓen Iji-Anyigba.

    BBC
  13. Mutane sun fusata a Legas saboda rashin kai masu kayan zaɓe

    BBC

    Yayin da ake ƙoƙarin rufe shiga layin zaɓe ga masu zaɓe a wasu sassan Najeriya, wasu mazaɓu na kukan ba a kai musu kayan zaɓen ba.

    Mazaɓar Amuwo Odofin da ke Legas, rumfa mai lamba 053 da 054 ba a kai kayan zaɓe a kan kari ba, inda mutane suka fusata, tare da zargin cewa ana ƙoƙarin yin maguɗin zaɓe.

    Jami'an tsaro sun hallara a yankin inda suka buƙace mutanen da su kwantar da hankula.

    BBC

    Gabanin wannan wasu rumfunan sun riƙa fuskantar matsalar na'urar BVAS wadda ke ƙin ɗaukar zanen yatsa da kuma fuska.

    BBC

    An samu irin wannan matsalar a Maidguri a Jihar Borno, ka zalika Gwamnan Jihar Rivers Wike ma da farko sai da na'urar taƙi ɗaukar fuskarsa.

    BBC
    BBC
  14. Hoto: Tsohon shugaban ƙasar Najeriya Olusegun Obasanjo ya kaɗa ƙuri'arsa

    Hotunan yadda tsohon shugaban ƙasar Najeriya, Olusegun Obasanjo ya kaɗa ƙuri'arsa a jihar Ogun.

    BBC
    BBC
    BBC
  15. Gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike ya kasa kaɗa ƙuri'arsa

    bbc

    Gwamnan Jihar Rivers Nyesom Wike ya gaza kaɗa ƙuri'arsa saboda kalubalen na'urar Bvas mai tantance masu kaɗa ƙuri'a.

    Masu aikin zaɓen daga INEC sun shawarce shi da ya koma gida daga baya sai ya je ya yi zaɓen, yayin da su kuma suka kira masu gyara na'urar.

    Gwamnan ya je wurin ne tare da matarsa Justice Eberechi Suzzette Nyesom-Wike, domin kaɗa ƙuri'ar tasa a mazaɓar Rumuepirikom da ke ƙaramar hukumar Obio Akpor.

    Ya nuna rashin jin daɗinsa game da wannan na'ura da ke tantance mutum da ɗan yatsa ko kuma da fuska, game da yadda ta gaza aiki.

  16. Peter Obi ya kaɗa ƙuri'arsa

    Ɗan takarar shugaban ƙasa ƙarƙashin jam'iyyar Labour Peter Obi, ya kaɗa kuri'arsa a jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya.

    'Yan jarida ne suka cika rumfar zaɓen dan takarar da ke Agulu, domin ɗaukar yadda Obi zai kaɗa kuri'ar.

    Mista Obi, ana masa kallon shi ne mutum na uku mai tarin magoya baya da suke neman takarar shugabancin ƙasar.

    Kamar sauran 'yan takarar Obi ma ya halarci wajen zaɓen tare da uwar gidansa.

    BBC
    BBC
    BBC
    BBC
  17. Yadda Kwankwaso ya kaɗa ƙuri'arsa a garin Madobi na jihar Kano

    Ɗan takara shugaban ƙasa na jam'iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Rabi'u Musa Kwankwaso ya kaɗa ƙuri'a a mazaɓarsa da ke ƙaramar hukumar Madobi a jihar Kano.

    Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano na ɗaya daga cikin ƴan takarar shugabancin ƙasa da ake ganin za su taka rawar gani a zaɓen na 2023.

    Ya fito ne da misalin ƙarfe 11:30 na safe, inda ya kaɗa ƙuri'ar tasa.

    Zaɓen Najeriya
    Zaɓen Najeriya
    Bayanan hoto, Kwankwaso dai na cikin 'yan takara na gaba-gaba da ake ganin za a fafata da su a zaɓen Najeriya na 2023.
    Zaɓen Najeriya
  18. Yadda ƴan gudun hijira suka yi dafifi domin kaɗa ƙuri'a a Yola

    Yayin da ake ci gaba da zaɓe a Najeriya, nan wasu 'yan gudun hijira ne suka yi dafifi domin kaɗa ƙuri'arsu a rumfar zaɓe da ke makarantar firamare ta Malkohi 009 a birnin Yola.

    Rumfar zaɓen tana da mutum 1,228 da suka yi rajista domin yin zaɓe.

    Sai dai, yawancinsu a wannan rumfar sun kasance ƴan gudun hijira ne.

    Polling Unit
    Rumfar zaɓe
    Polling Unit
    Bayanan hoto, Hadiza Abubakar

    "Na fito inyi zabe ne saboda in kawo gwamnati da za ta mayar da ni garina Gwoza, in ji Hadiza Abubakar, 'yar gudun hijira da ke zaɓe a rumfar zaɓen da 'yan gudun hijira ke kaɗa kuri'a na makarantar Malkohi a Yola.

    Matar dai, mai shekara 40 ta kuma ce tana da yara 8. Ta ce ta bar Gwoza shekaru 8 da suka gabata.

    Ta hau layin zaɓe tun karfe 7 na safe.

  19. Ko kun san abubuwan da ke lalata ƙuri'unku a lukutan zaɓe?

  20. Tinubu ya kaɗa ƙuri'arsa a Legas

    BBC
    Bayanan hoto, Tinubu ya fita da uwar gidansa domin kaɗa tasa ƙuri'ar

    Dan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar APC mai mulki Bola Ahmed Tinubu ya kaɗa ƙuri'arsa a mazaɓarsa ta Awolowo da ke Falomo da ke Legas.

    Da misalin ƙarfe 9:30 na safe ne dan takarar ya isa inda zai ƙaɗa kuri'ar tasa tare da mai ɗakinsa Oluremi Tinubu.

    An samu jinkiri gabanin fara kaɗa ƙuri'a a rumfar zaɓen, sai dai daga baya zaɓen ya kankama. Akwai mutum aƙalla 832 da suka yi rajistarsu a wannan rumfar zaɓe.

    BBC
    BBC
    BBC
    Bayanan hoto, 'Yan jarida da dama sun taru domin su yi wa Tinubu tambayoyi
    BBC
    BBC