Hukumar daƙile cututtuka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta ce an samu ƙarin mutum 1,301 da suka kamu da annobar korona a ƙasar ranar Talata.
A cewar hukumar ta NCDC, mutum 15 ne suka mutu cikin sa'a 24 da ta gabata sannan an sallami mutum 1,261 bayan sun warke daga cutar.
Bisa sabbin alkaluman hukumar, har yanzu jihar Legas ce ke kan gaba da mutanen da suka kamu da cutar cikin kwana ɗayan inda take da mutum 551.
Abuja, babban birnin ƙasar ne ke biye wa jihar Legas da mutum 209 sai Oyo mai mutum 83.
Jihar Plateau na da mutum 65 sai Kaduna mai 64 yayin da a Enugu aka samu ƙarin mutum 61 da suka kamu da cutar ranar Talata.
Jihar Rivers na da 44 sai Ondo mai 39, Benue kuma tana da 37 inda a Akwa Ibom aka samu mutum 31.
Kano na da 19 sai Delta da Gombe masu 18 kowace jiha. Ogun na da 16, Edo 15, Kebbi 10, Ebonyi 9.
Jigawa 4, Osun 3, Zamfara 3, Borno 1 sai Nassarawa 1.
Yanzu dai kididdigar masu cutar a Najeriya ita ce 113,305 sannan mutum 91,200 sun warke inda kuma mutum 1,464 suka rasu