El-Rufa'i: Abin da ya sa na tsawaita dokar kulle da mako biyu a Kaduna

Elrufai

Asalin hoton, @GOVKADUNA

Bayanan hoto, El-Rufai ya sha alwashin babu wanda zai shigar masa jiha daga Kano yayin bikin Sallah
An wallafa

Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufa'i ya tsawaita dokar zaman gida a jihar da mako biyu gaba, bayan shafe kwanaki 60 ana cikin yanayi na hana zirga-zirga

A wata sanarwa da mataimakiyar gwamnan, Dr, Hadiza Balarabe ta yi, ta ce za a bai wa wasu bangarori damar dawo da ayyukansu sannu a hankali.

Sai dai babu wani karin bayani kan ka'idoji ko matakan dawo da hada-hada ko wasu ayyukan da gwamnatin ta bayyana.

Jihar Kaduna na cikin jihohin arewacin Najeriya da annobar korona ke yi wa barazana abin da yasa gwamnata daukan matakai cikin hanzari don dakile yaduwarta.

A jimillace mutum 208 ne suka kamu da cutar a Kaduna, sai dai kamar yadda gwamnan ya shaida akasari aljamirai ne da aka dawo dasu jihar daga Kano.

Karin bayani kan coronavirus

Gwamnan El-Rufa'i ya tashi haikan domin yakar wannan annoba dalilan da yasa yake daukan matakan da al'ummar jihar ke ganin akwai takurawa.

Malam El-Rufai, ya shafe ranakun Juma'a da Asabar a kan iyakar Kaduna da Kano domin tabbatar da dokar hana zirga-zirga tsakanin jihohi.

Da ma El-Rufai ya lashi takobin cewa babu wanda zai shigar masa jiha daga Kano, biyo bayan matakin da Gwamnan Kano Abdullahi Ganduje ya ɗauka na ci gaba da yin sallar Juma'a da kuma ta Idi a Kanon.

Sanarwar da gwamnan Kaduna ya yi a yanzu na zuwa ne bayan cikin makon daya gabata mataimakiyarsa ta ce har yanzu basu gamsu da yanayin da cutar take a jihar ba ballantana su bude jihar.

Gwamna El-Rufai shi ne mutum na farko da cutar ta kama a jiharsa ta Kaduna, amma ya sanar da warkewa daga cutar ranar Laraba 22 ga watan Afrilu bayan ya kamu da korona ranar 28 ga watan Maris.

Gwamnatin Kaduna kuma ta ce za ta tilasta amfani da abin rufe fuska saboda muhimmancinsa wajen rage yaduwar cutar tsakanin mutane da kuma kare lafiyar jama'a.

BBC