Trump ya ce Iran za ta dandana kudarta

EPA

Asalin hoton, EPA

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1

Magoya bayan Iran masu zanga-zanga a Iraki sun fara kafa tantuna da niyyar zaman dirshen a gaban ofishin jakadancin Amurka da ke birnin Bagadaza.

Masu zanga-zangar sun bayyana cewa ba za su daina zanga-zangar ba, kuma ba za su bar gaban ofishin jakadancin ba har sai sojojin Amurka sun fice daga Iraki.

A ranar Talata ne wasu masu zanga-zanga suka cinna wuta a wasu sassan ofishin jakadancin Amurkar da ke Bagdaza biyo bayan wani hari ta sama da Amurka ta kai wa kungiyar mayakan sa-kai da Iran ke goya wa baya a Iraki.

Kimanin mayaka 25 ne suka mutu lokacin da Amurkan ta kai hare-haren a sansanin mayakan masu alaka da kungiyar Kataib Hezbollah a Iraki da Syria ranar Lahadi.

Harin saman da Amurkar ta kai na zuwa ne jim kadan bayan wasu hare-haren roka da aka kai wa sojojin Amurka wanda harin ya yi sanadiyar mutuwar wani farar hula Ba'Amurke.

Jagoran addini a Iran Ayatollah Ali Khamenei ya caccaki Shugaba Trump bayan Trump din ya zargi Iran da kai hare-haren.

Jami'ai a Amurka sun bayyana cewa akwai dakarun kasar da dama da za a kara turawa zuwa yankin na Iraki sakamakon tayar da zaune tsaye da ake samu.

Ko a wasu jerin sakonnin Twitter da Trump din ya wallafa na murnar sabuwar shekara ya bayyana cewa Iran din za ta dandana kudarta sakamakon harin da ta kai.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

Ya bayyana cewa sai ta ''gane kurenta'' dangane da hare-haren, inda ya ce ''wannan ba kashedi ba ne, barazana ce. Barka da Sabuwar Shekara."