United za ta yi wasa a Malaysia da Hong Kong idan an kare kakar bana

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1

Manchester United za ta buga wasanni a Malaysia da Hong Kong da zarar an kammala gasar Premier League a watan Mayu.

United za ta kara da fitattun ƴan wasan Asia a Kuala Lumpur ranar 28 ga watan Mayu daga nan ta ziyarci birnin Hong Kong kwana biyu tsakani.

United za ta ziyarci nahiyar Asia da zarar ta buga wasan karshe a gida da Aston Villa a Premier League ranar 25 ga watan Mayu.

Ana sa ran United za ta samu kuɗi da zai kai £7.8m a ziyar da za ta kai da wasannin da za ta buga a Asia.

Daga nan kuma ƙungiyar da Ruben Amorim ke jan ragama, za ta je Amurka daga ranar 26 ga watan Yuli zuwa 3 ga watan Agusta, domin buga wasannin tunkakar kakar baɗi.

United tana da magoya baya da yawa a Malaysia, kuma tana da hulɗar zirga-zirga da kamfanin jirgin sama na Malaysia.

Rabon da United ta ziyarci Malaysia tun 2009, wadda ta buga wasanni a Hong Kong a 2013.

A bara kan fara kakar bana, Tottenham da Newcastle United, sun yi wasanni a Austalia.

Har yanzu ana ta kukan cewar wasa yana yi wa ƴan ƙwallo yawa, bayan da aka kara yawan ƙungiyoyi a Fifa Club World Cup, an kara wasanni a Champions League da sauran gasar Turai.

Hakan ne ya sa Ingila ke buga wasa zangon farko a FA Cup, maimakon gida da waje da ake yi a baya, domin a rage yawan wasannin da ƴan ƙwallo ke buga wa.