Man City za ta sake ɗaukar Gundogan daga Barcelona

Asalin hoton, Getty Images
Manchester City tana kokarin sake ɗaukar Ilkay Gundogan daga Barcelona.
Mai shekara 33 ya bar Etihad zuwa Barcelona a 2023, bayan da kwantiraginsa ya kare, wanda shi ne ƙyaftin lokacin da ƙungiyar ta lashe kofi uku a tarihi.
Ƙungiyar da ke buga La Liga na fama da matsin tantalin arziki, wadda ta kasa kammala cinikin Dani Olmo daga RB Leipzig da ta ɗauka a bana - hakan ya sa za ta rabu da ɗaya daga cikin masu karɓar albashi da yawa.
City ta sayar da Julian Alvarez ga Atletico Madrid kan £81m a bana, sannan Oscar Bobb zai yi jinyar wata huɗu, kenan Gundogan yana da rawar da zai taka.
Tun farko Pep Guardiola bai so Gundogan ya bar City ba a karshen kakar bara, amma yanzu ƙungiyar a shirye take ta sake ɗaukar ɗan wasan.
Bayan da ya koma City daga Borussia Dortmund kan £20m a 2016, Gundogan ya buga wasa 304 da cin ƙwallo 60.
A kaka bakwai da ya yi a Etihad ya lashe kofi 14 daga ciki Premier League biyar da Champions League da FA Cup biyu da Carabao huɗu.
Haka kuma ya ɗauki Community Shields biyu.










