Super Eagles za ta buga daf da karshe na 16 a Afcon 2023

An wallafa

Najeriya za ta buga zagayen daf da karshe karo na 16 a gasar kofin Afirka da Ivory Coast ke karbar bakunci da ake kira Afcon 2023.

Hakan ya sa ta yi kan-kan-kan da Masar a jerin kasashen da suka kai zagayen daf da karshe da yawa a gasa hudu baya a wasannin.

Super Eagles ta samu matakin ne, bayan da ta ci Angola 1-0 ta hannun Ademola Lookman ranar Juma'a 2 ga wwatan Fabrairu.

Najeriya wadda ke buga Afcon karo na 20, za ta kara a zangon daf da karshe sau 16, iri daya da bajintar Masar, wadda ta fafatawa a gasar karo 26.

Tawagar Ghana ta halarci Afcon a Ivory Coast gasa ta 24 da ta kara a wasannin, wadda ta kai zagayen daf da karshe har sau 14 da daukar kofi hudu.

Ƙasar Kamaru da Ivory Coast sun samu buga gurbin daf da karshe a babbar gasar tamaula ta Afirka sau 10 kowacce.

Koda yake sau uku Najeriya ta dauki Afcon, Masar ce kan gaba a yawan lashe kofin mai bakwai jimilla da Kamaru mai biyar.

Wasannin daf da karshe a Afcon 2023

Ranar Laraba 7 ga watan Fabrairu

  • Najeriya da South Afirka
  • Jamhuriyar Dimuƙuraɗiyyar Congo da Ivory Coast.