Gabriel Jesus ya kawo karshen kamfar cin kwallo a Arsenal

Gabriel Jesus

Asalin hoton, Getty Images

An wallafa

Arsenal ta ci gaba da jan ragamar teburin Premier League da tazarar maki takwas tsakaninta da Manchester City ta biyu.

Gunners ta doke Leeds United 4-1 a wasan mako na 29 a babbar gasar tamaula ta Ingila da suka kara ranar Asabar a Emirates.

Gabriel Jesus ne ya ci biyu daga ciki, karon farko da ya ci wa Arsenal kwallo tun cikin Oktoba a wasan da Gunners ta ci Tottenham 3-1 a Premier League.

Dan wasan tawagar Brazil ya ci wa Gunners kwallo biyar a wasa takwas da ya fara yi tun bayan da ya koma Emirates daga Manchester City a Yulin bara.

Tun daga nan bai sake cin kwallo a Arsenal ba a dukkan fafatawa har sai wasan hamayya da Tottenham a Lik.

Ranar Asabar aka fara wasa da Jesus a Arsenal a tamaula, bayan da ya sha jinya sakamakon raunin da ya ji a gasar kofin duniya a tawagar Brazil a Qatar a 2022.

To sai dai ya shiga canji a karawar da Gunners ta casa Crystal Palace 4-1 a wasan Premier League ranar 19 ga watan Maris.

Tun kan nan ya fuskanci Fulham a League Cup, wanda ya yi minti 13, ya buga wasa da Sporting minti 45, sannan da Crystal Palace.

Gabriel Jesus ya zura kwallo 52 a raga a Premier League a City da Arsenal, daga ciki aka yi nasara 49 da canjaras uku a ranar da ya ci kwallayen.

Gabriel Jesus ya buga kwallo zuwa raga sau 42 a wasa 17 a Premier League a kakar nan, yayin da 23 daga ciki suka nufi raga kai tsaye.

Arsenal wadda ke fatan lashe Premier League a bana a karon farko tun bayan 2003/04 ta bai wa City tazarar maki takwas, saura wasa tara a kare kakar nan.