Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
An naɗa Usman Abdallah a matsayin sabon kocin Kano Pillars
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta sanar da naɗin tsohon mataimakin kociyan Super Eagles Usman Abdallah a matsayin sabon wanda zai jagoranci tawagar ƴan wasanta.
Sashen yaɗa labarai na kulob ɗin ya sanar da nadin Abdallah a shafinta na dandalin X da safiyar Juma'a.
Sanarwar ta ce :“Mun yi farin cikin sanar da cewa mun cimma yarjejeniya bisa manufa don naɗa Usman Abdallah a matsayin sabon jagoran tawagar ƴan wasan mu. Ku kasance da mu don samun cikakkun bayanai kan kwantiragin da sauran abubuwan da ƙungiyar ta sanya a gaba.”
Abdallah zai maye gurbin Paul Offor, wanda aka sallama wata guda bayan an naɗa shi.
Abdallah ya taɓa lashe kofin gasar NPFL ta Najeriya da Enyimba a shekarar 2019 ya kuma kai wasan kusa da na ƙarshe a gasar cin kofin CAF confederations Cup.