Shin ficewar jiga-jigan NDC a Kano za ta karya lagon Kwankwasiyya?

Kwankwaso
An wallafa
Lokacin karatu: Minti 3

Ana ci gaba da tattaunawa kan sabuwar ɓarakar da ake ganin ta sake kunno kai a jihar Kano, musamman bayan Sanata Rufa'i Sani Hanga ya fice daga Kwankwasiyya duk da cewa shi ne mai riƙe da babban muƙami a tsarin a yanzu.

Sanata na daga cikin ƴan majalisar dokokin Najeriya daga jigar Kano da suka ci gaba da kasancewa tare da Kwankwaso tun bayan ficewar Gwamna Abba Kabir daga jam'iyyar NNPP zuwa APC.

A farkon shekarar nan ne Kwankwaso da mutanensa ciki har da Sanata Hanga suka fice daga NNPP zuwa ADC, daga baya kuma suka koma NDC.

A shekarar 2023 ne aka zabi Sanata Rufai Sani Hanga a matsayin ɗanmajalisar dattawan Najeriya mai wakiltar Kano ta Tsakiya a jam'iyyar NNPP kwankwasiyya.

A baya-bayan nan an ga Sanata Hanga na ganawa da wasu jiga-jigan APC, ciki har da shugabanta na kasa da Gwamna Abba, a wani mataki da masu sharhin siyasa ke ganin kamar zai bar tafiyar Kwankwasiyya.

Haka kuma an ga sanatan tare da tsohon gwamnan jihar, Kabiru Gaya suna ganawa da shugaban jam'iyyar na ƙasa.

A wata tattaunawa da ya yi da BBC Hausa, Sanata Kabiru Gaya ya ce shugaban ƙasa ya nemi su koma APC, duk da ya nanata cewa shi ba zai yi wata magana game da abin da ya faru tsakaninsa da tsarin Kwankwasiyya ba.

Ficewar za ta taɓa lagon Kwankwasiyya?

Dr Kabiru Sa'id Sufi Malami a Kwalejin Share Fagen Shiga Jami'a da ke Kano, kuma mai shairhi kan al'amuran siyasar Najeriya ya ce dole ficewar manyan siyasa a kusa da lokacin zaɓe ya taɓa kowace irin jam'iyya ce.

Ya ce su biyu da suka fice a yanzu ba matsayinsu ɗaya ba, inda ya ƙara da cewa dukkansu kowanne yana da yanayin nauyinsa.

"Shi Kabiru Gaya daga baya ya shiga tsarin kuma babu tabbacin irin ɗimbin magoya baya da ya tafi kamar Sanata Rufai Hanga wanda shi ne sanata ɗaya tilo da Kwankwasiyya ke da shi a Kano," in ji shi.

Ya ƙara da cewa ana gani ko a kafafen sadarwa Sanata Rufai Hanga yana tara mabiya.

"Kuma a siyasa idan aka fita dole a ji ba daɗi, kuma idan aka lura dukkansu tsofaffin ƴan siyasa ne kuma suna da tasiri, musamman shi Kabiru Gaya da tsohon gwamna ne."

Masanin siyasar ya ce wannan ne ya sa fitarsu a wannan lokaci zai iya haifar da matsala ga tafiyar ta Kwankwasiyya.

"Kuma idan aka yi lakari da zaɓe na ƙara ƙaratowa, kowace jam'iyya neman ƙari take yi ba rashi ba, don haka za a iya cewa NDC ta yi rashin jiga-jigai kuma wataƙila da mabiya masu yawa."

Fita daga Kwankwasiyya

Tsallake Whatsapp
Tasharmu ta WhatsApp

Yanzu za ku iya samun labaran BBC Hausa kai-tsaye a wayoyinku.

Latsa nan domin shiga

Karshen Whatsapp

Wani abu da ake kwatantawa shi ne zubin yanayin tsarin lokacin zaɓen mai zuwa da na baya, musamman zaɓen shekarar 2019.

A game da wannan kwatancen, Kabiru Sufi ya ce akwai kamanceceniya ta hanyoyi da dama.

"Gaskiya akwai yanayi kusan iri ɗaya duba da cewa ya faru lokacin da ake tunkarar zaɓe."

Masanin harkokin siyasar ya ce a duk lokacin da aka ce zaɓe ya kusa, jam'iyyu ko tafiyar siyasa ƙari suke buƙata ba raguwa ba.

Wannan ne ya sa Kabiru Sufi yake ganin ficewar na iya taɓa ƙarfin tsarin na Kwankwasiyya.

"Wannan na iya shafar tagomashin tafiyar a idanun al'umma musamman saboda irin ƙorafe-ƙorafen wasu da suke fice, wanda kuma hakan zai iya shafar masu so su shiga saboda za su yi tunanin ba lallai su samu mafita ba saboda yawan ƙorafin masu ficewar," in ji shi.

Wani abu da wasu ke magana shi ne me ya sa ake yawan fita daga tsarin Kwankwasiyya duk da cewa ba sabon abu ba ne a siyasar Najeriya.

A game da wannan, Kabiru Sufi akwai yanayin tsarin tafiyar da kuma buƙatun ƴan siyasa.

"Ƴansiyasa mafi yawa idan baƙatarsu ba ta biya ba, ba dole ba ne su ci gaba da zama a tsarin da suke ciki."

Ya ce wasu suna tunanin Kwankwasiyya da ake cewa "amana tana da tsarin shugaba ne. Don haka akwai rashin fahimtar tsarin saboda tsari ne ne da ke da biyayya ga shugabanci."

Sufi ya ce a tsarin shugabancin ne wasu ke ganin wannan yanke hukuncin da shugaba yake yyi suke kallo a matsayin kama-karya.

"Musamman idan ba su samu abin da suke so ba, amma idan sun samu yadda suke so ba sa damuwa. Saboda haka ne wasu suke gani ko dai rashin fahimtar tsarin ko kuma lokacin da suka ga ba su samu abin da suke so ba ne suke tutsu," in ji shi.