Henderson ya koma Al-Ettifaq ta Saudi Arabia

An wallafa

Kyaftin din Liverpool, Jordan Henderson ya koma Al-Ettifaq mai buga babbar gasar tamaula ta Saudi Arabia.

Dan kwallon tawagar Ingila, mai shekara 33 ya amince da kunshin yarjejeniyar fam miliyan 12 har da karin tsarabe-tsarabe.

A sakon ban kwana da ya yi wa Liverpool, ya ce zai bar kungiyar inda ya yi kaka 12, wadda ya lashe Premier League da Champions League a ita da sauran nasarori.

Henderson yana Liverpool tun bayan da ya koma Anfield daga Sunderlandn kan fam miliyan 20 a watan Yunin 2011.

Ya buga karawa 492 da cin kwallo 33 da bayar da 57 aka zura a raga ya kuma dauki kofi bakwai a Liverpool.

Henderson zai yi aiki a karkashin Steven Gerrard, wanda shine kociyan Al-Ettifaq.

Mutanen biyu sun taka leda tare a Liverpool daga baya Gerrard ya bar Anfield a 2015.

Henderson ya zama kyaftin din Liverpool a 2015, wanda ya ja ragama ta lashe Champions League a 2019 daga baya ta dauki Uefa Super Cup da Fifa Club World Cup a kakar gaba.

Haka kuma Al-Ittihad ta taya wani dan wasan Liverpool, Fabinho kan fam miliyan 40 ranar 14 ga watan Yuli.