Ku San Malamanku tare da Malam Mu'azzam Sulaiman Khalid

Ku San Malamanku tare da Malam Mu'azzam Sulaiman Khalid
An wallafa

Shirin Ku San Malamanku na wannan makon ya karɓi baƙuncin Malam Muazzam Sulaiman Khalid, wanda aka haifa a Unguwar Soron-Ɗinki da ke Jihar Kano.

Malamin ya taso tare da fara karatunsa na allo a cikin garin na Kano a hannun yayan mahaifinsa Malam Datti.

Ya yi karatun Islamiyya a wajen mijin yayarsa mai suna Malam Ibrahim Ci gari. Kazalika, ɗan uwansa ma ya koya musu littafin Kawa'idi.

Ya fara karaunsa na firamare a makarantar Sheikh Nasiru Kabara, shugaban Ɗariƙar Ƙadiriyya a Kano, yayin da ya yi sakandaren koyon Larabci ta SAS.

Malamin ya samu shaidar difiloma daga kwalejin shari'a ta Aminu Kano kafin daga bisani ya samu tallafin karatu a Jami'ar Musulunci ta birnin Madina da ke Saudiyya.

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton, Malam Muazzam na dab da kammala digirinsa na uku.