Ra'ayi Riga: Kan matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta a Najeriya 15/03/2025

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1

A shirinmu na Ra'ayi Riga wannan makon, mun nazari ne kan batun yara waɗanda ba sa zuwa makaranta a Najeriya.

A kwanakin baya ne dai asusun kula da ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya ya sake nanata cewa akwai adadin yara masu yawan gaske waɗanda ba sa zuwa makaranta a jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Shin me yake kawo wannan matsalar?

Wane mataki gwamnatin take ɗauka?

Shin laifin waye?

Me ya kamata a yi?

Waɗannan na daga cikin batutuwan da muka tattauna a cikin shirin namu na Ra'ayi Riga na wannan makon.