Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya kai ziyara birnin Maiduguri na jihar Borno a arewa maso gabashin ƙasar, ranar Alhamis 18 ga watan Agustan 2022.
Jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar ta yi fama da ricikin Boko Haram, abin da ya sa dubban jama’a suka shiga mawuyacin hali.
Wannan dai ita ce ziyara ta uku da shugaban ya kai jihar Borno cikin shekara guda.
Ga wasu zaɓaɓɓun hotuna na yadda ziyarar ta kasance.
Asalin hoton, Presidency
Asalin hoton, Presidency
Bayanan hoto, Ma'aikatar jin ƙai da ci gaban al'umma da kare aukuwar bala'i ce ta gayyaci Shugaba Buhari, a wani ɓangare na bikin ranar jin ƙai ta duniya.
Asalin hoton, Presidency
Bayanan hoto, Shugaba Muhammadu Buhari ya kaddamar da wasu ayyuka da suka haɗa da gidajen malaman makaranta da aka kammala aikinsu.
Asalin hoton, Borno Govt
Bayanan hoto, Rukunin gidajen malamai da gwamnatin Borno ta gina a Bulumkutu na daga cikin ayyukan da shugaban ya ƙaddamar
Asalin hoton, Borno Govt
Bayanan hoto, Wannan ita ce ziyara ta uku cikin shekara guda da Shugaba Buhari ke kai wa jihar Borno.
Asalin hoton, Borno Govt
Bayanan hoto, A daya daga cikin ziyarar da shugaban ya kai jihar Bornon ne ya bayar da umarnin gina gidaje 10,000 don tsugunar da ƴan gudun hijirar da rikicin Boko Haram ya raba da muhallansu.
Asalin hoton, Presidency
Bayanan hoto, Kuma a ziyarar wannan karon Shugaba Muhammadu Buharin ya ƙaddamar da 500 daga cikinsu.
Asalin hoton, Presidency
Bayanan hoto, Hukumomin jihar Borno sun ce za a kammala gina gidaje 6,000 ɗin nan ba da jimawa ba.