Arsenal da Newcastle na gogayya kan Mohammed Kudus

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta West Ham na da niyyar sayar da ɗan ƙwallon Ghana Mohammed Kudus idan ta samu "babban tayi" a watan Janairu, kamar yadda shafin TalkSPORT ya ruwaito.

Rahoton ya ce Arsenal na duba yiwuwar sayen ɗanwasan tsakiyar, wanda ke da farashin fam miliyan 85 a ƙunshin yarjejeniyarsa da Hammers ɗin.

Sai dai kuma, akwai yiwuwar sai Arteta ya sayar da wasu 'yanwasan kafin ya iya sayen Kudus.

A gefe guda kuma, Newcastle United na shirin fafatawa da Arsenal ɗin da ma Liverpool wajen saye Kudus, a cewar rahoton Daily Express.

Rahoton ya nuna cewa Hammers ta yi wa ɗanwasan kuɗi fam miliyan 90, yayin da Newcastle ke da niyyar gwada sa'arta a kansa.

Kudus na cikin manyan 'yanwasan West Ham duk da cewa ƙwallo biyu kawai ya ci zuwa yanzu tare da bayar da ɗaya a zira a raga a kakar wasa ta bana.