Ku San Malamanku tare da Malam Saminu Ɗorayi

Ku San Malamanku tare da Malam Saminu Ɗorayi
An wallafa

Filin Ku San Malamanku na wannan makon ya karɓi baƙuncin Malam Saminu Ibrahim Ɗorayi, wanda shi ne babban limamin masallacin Ɗorayi Babba a Jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya.

An haifi malamin a garin Kano a shekarar 1940 - yana da shekara 82.

Malamin ya ce bai yi maraicin karatu ba saboda yawan almajiran mahaifinsa, inda limamin Ɗan-Bare Malam Halilu da limamin Ɗorayi Malam Sani suka fi yin fice.

Ya ƙara da cewa a hannunsu ne ya yi karatu mai yawa bayan ya sauke Al-Ƙur'ani mai tsarki a hannun mahaifinsa.

"Na ji ciwo da ɓacin rai lokacin da na ga ana kallon malaman-soro a matsayin ba komai ba - ba ka da wani abu idan ba karatun shaida ka yi ba," a cewar shehin malamin.

"Wannan dalilin ya sa na ce 'bari mu yi karatun nan na takarda, ko dai ba mu samu boko ba ma samu shahada [shaidar karatu]'.

"Sai na shiga SAS (kwalejin harshen Larabci). Bayan na gama kuma na shiga Jami'ar Bayero, inda a nan na yi difiloma da digiri."