Martinez zai yi jinya har ƙarshen kaka

Asalin hoton, Getty Images
Ɗanbayan Manchester United Lisandro Martinez ba zai sake taka leda ba a sauran wasannin kakar nan saboda raunin da ya ji a guiwarsa, a ranar Lahadi.
An fitar da ɗanwasan ne mai shekara 27, a karawar da United ta yi rashin nasara a gida a hannun baƙinta Crystal Palace, raunin da tun a lokacin kociyan ƙungiyar Ruben Amorim ya bayyana a matsayin babbar matsala.
A ranar Alhamis ƙungiyar ta ce har yanzu ana duba yanayin raunin domin sanin yadda ya fi dacewa a yi masa magani da kuma tsawon lokacin da zai ɗauka yana jinya.
Sanarwar ta ce kowa a ƙungiyar yana yi wa Lisandro Martinez fatan warkewa sarai, kuma za su ci gaba da tallafa masa a kodayaushe.
Rashin Martinez babban ƙalubale ne ga Amorim wanda ke fama kan ganin ya dawo da ƙungiyar ta Old Trafford kan ganiyarta.
Yanzu United tana ta 13 a teburin Premier bayan kashin da ta sha a hannun Palace - rashin nasarar da shi ne na bakwai a wasa 13 na gida a bana.
A gobe Juma'a ne United za ta karɓi baƙuncin Leicester City, a karawar zagaye na huɗu ta cin kofin FA.
Martinez ya tafi jinyar ne yayin da United ɗin ke ɗari-ɗarin dawo na Luke Shaw, da ake ganin bai gama warkewa ba sarai, daga raunin da ya ji na ƙarshe.















