Gerrard ya tsawaita kwangilarsa a Al-Ettifaq ta Saudiyya

Asalin hoton, getty
Steven Gerrard ya sanya hannu a yarjejeniyar ci gaba da jan ragamar kungiyar Al-Ettifaq ta Saudiyya inda zai ci gaba tare da su har zuwa shekara ta 2027.
A kakar wasan da ta wuce ne, tsohon kocin Aston Villa ya koma jagorantar tawagar wadda ke murza leda a gasar Saudi Pro League.
A yanzu haka dai Al-Ettifaq ce ta takwas a kan teburin gasar kwallon kasar, a yayin da Al-Hilal wadda ke saman tebur ta bai wa Al-Ettifaq tazarar maki 28.
Wannan sanarwar na zuwa ne bayan da dan kwallon Ingila wanda ke wasa a Al-Ettifaq, Jordan Henderson ya koma kungiyar Ajax ta Netherlands.
Gerrard na daga cikin masu horas da 'yan kwallo da suka fi karbar albashi a duniya inda yake samun fan miliyan 15 a duk shekara.
A cikin wata sanarwa tsohon kyaftin din Ingila ya ce "Wannan abin farin ciki ne gare ni da iyalaina sannan alama ce ta nuna godiya saboda kokarin dana ke yi".
Steven Gerrard ya samu nasara a wasanni bakwai cikin 21 a matsayinsa na manajan Al-Ettifaq.







