Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Pillars ta ragargaji Nasarawa United
Kano Pillars ta doke Nasarawa United ta ci 3-0 a wasan mako na shida a gasar cin kofin Firimiyar Nigeria da suka fafata a Sani Abacha da ke kofar Mata a Kano, Nigeria.
Pillars ta ci kwallayen ne tun kan a je hutu ta hannun Adamu Hassan wanda ya ci biyu a karawar, sannan Chinedu Sunday ya zura daya a raga.
Wannan shi ne wasa na biyu da kocin Pillars Ibrahim Musa ya ja ragamar kungiyar tun bayan da ya sake komawa kan aikin koci, bayan da aka sallame shi a bara.
Kawo yanzu Pillars ta ci wasa biyu da canjaras biyu aka doke ta karawa biyu, tana da maki takwas kenan kawo yanzu.
Sauran sakamakon wasannin mako na shida:
- MFM 1-0 Wikki
- Enyimba 2-0 Rivers Utd
- Sunshine Stars 2-1 Remo Stars
- Katsina Utd 3-1 Tornadoes
- El-Kanemi 2-1 Yobe Stars
- Akwa Utd 3-0 Go Round
- Gombe Utd 0-0 Plateau Utd
- Heartland 3-2 Kada Stars
- FCIU 1-2 Abia Warriors