Duniya ta kyamaci juyin mulkin Thailand

Asalin hoton, Reuters
An wallafa
Kasashen duniya sun yi Allah-wadai da juyin mulkin da sojoji suka yi a kasar Thailand.
Sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry ya ce babu dalilin yin juyin mulki.
Shi ma sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya Ban ki-Moon ya yi kiran da a gaggauta dawo da Dimokradiyya kasar; kamar yadda mai magana da yawunsa Stephane Dujarric ya shaidawa BBC.
A bangare guda kuma gwamnatin Sojin kasar ta bukaci tsohuwar Firai-Minista Yingluck Shinawatra da masu fada a ji a harkokin siyasar kasar da su bayyana a gabanta.








