Nan muka kawo karshe shirin.
Da fatan za ku tara ranar Juma'a domin kawo muku wani labarin wasanni kai tsaye daga BBC Hausa.
Sunana Mohammed Abdu Mamman Skeeper Tw ke yi muku fatan alheri.
Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye kan cefanen 'yan kwallo da labarin wasanni.
Mohammed Abdu
Nan muka kawo karshe shirin.
Da fatan za ku tara ranar Juma'a domin kawo muku wani labarin wasanni kai tsaye daga BBC Hausa.
Sunana Mohammed Abdu Mamman Skeeper Tw ke yi muku fatan alheri.
Kyaftin din Liverpool, Jordan Henderson ba zai buga wa kungiyar wasan sada zumunta da za ta kara da Karlsruher SC ba, bayan da ake ta batu kan makomarsa a Anfield.
Ana alakanta shi da zai koma Al Ettifaq, kungiyar da ke buga gasar Saudi Arabia, wadda Steven Gerrard ke horarwa.

Asalin hoton, Getty Images
Eddie Howe ya kwatanta wasan da Newcastle United ta ci Rangers 2-1 ranar Talata da cewar tamkar gasar zakarun Turai suka buga, saboda ingancin karawar a filin wasa na Ibrox.
Miguel Almiron da Harrison Ashby ne suka ci wa Newcastle kwallaye.

Asalin hoton, Getty Images
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Liverpool ba ta da shirin sayar da Luis Diaz, kamar yadda The Athletic ta wallafa.
Dan kasar Colombia ya koma Anfield da taka leda daga Porto a Janairun 2022, wanda yanzu ake alakanta shi da Al Hilal kan fam miliyan 43.3, kudin da ake ganin Liverpool za ta amince da tayin.
Tuni Liverpool ta bai wa dan kwallon riga mai lamba bakwai, wadda take fatan zai taka rawar gani a kakar 2023/24, wanda ya yi fama da jinya a kakar da ta wuce.
Diaz shine na uku daga Liverpool da ake alakanta su da komawa buga gasar Saudi Arabia, bayan Fabinho da kuma Jordan Henderson.

Asalin hoton, Getty Images
Manchester City ta amince ta sayar da Riyad Mahrez kan fam miliyan 30 ga Al-Ahli.
Mai shekara 32 an bashi izinin da kada ya bi City wasannin sada zumunta da za ta buga a Japan da kuma Koriya ta Kudu.
Tuni dai City ta amince da tayin da aka yi wa dan kwallon Algeria, wanda darajar dan kwallon ta yi daidai da shi, wanda saura kaka biyu yarjejeniyarsa ta kara a Etihad.

Asalin hoton, Getty Images
Wayne Rooney ya ce shekara biyar mai zuwa ita ce da Marcus Rashford ya kamata ya nuna kansa a fagen taka leda a duniya tare da Mancheste United.
A makon nan Rashford ya saka hannu kan kwantiragin da zai ciga da taka leda a Old Trafford har zuwa karshen kakar 2028.

Asalin hoton, Getty Images
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Zeki Amdouni[Daga Basel zuwa Burnley]
Benie Traore[Daga Hacken zuwa Sheffield United]
English Football League
Ethan Ampadu[Daga Chelsea zuwwa Leeds] kan fam miliyan bakwai
James Balagizi[Daga Liverpool zuwa Wigan] Wasannin aro zai buga
Abu Kamara[Norwich - Portsmouth] Wasannin aro zai buga
Viljami Sinisalo[Aston Villa - Exeter] Wasannin aro zai buga
Joseph Hungbo[Daga Watford zuwa FC Nurnberg]
Wasu cinikin da bai shafi Premier League ba
Benjamin Mendy[ Zuwa Lorient]
Oriol Romeu[Daga Girona zuwa Barcelona]
Eddie Howe ya yi magana kan makomar Allan Saint-Maximin a Newcastle, wanda bai yi wa kungiyar wasan sada zumunta da ta ci Rangers 2-1 ba ranar Talata, wanda aka ce da kyar idan zai je Amurka wasannin da za ta buga.

Asalin hoton, Getty Images
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya, Gianni Infantino ya ce wasan tamaular mata na samun cin gaba tun daga shekara goma da ta wuce.
Ya kuma ce yana da kwarin gwiwa cewar masu sukar wasannin za su yi matukar son gasar kwallon kafa ta mata nan gaba.
Fifa na sa ran mutum biliyan biyu ne za su kalli gasar kofin duniya ta mata da za a fara a ranar Alhamis a Aucland da za a yi fafatawa 64 da Australia da New Zealand za su karbi bakunci.
Kasashe hudu ne daga Afirka da za su wakilce ta da suka hada da Morocco da Zambia da Nigeria da Afirka ta Kudu mai tawagar da ake kira Banyana Banyana.
Manchester United ta doke Lyon 1-0 a wasan sada zumunta, kuma Donny van de Beek ne ya ci mata kwallon bayan da suka koma zagaye na biyu a karawar.
United za ta ziyarci Amurka domin buga wasan sada zumunta da Arsenal.

Asalin hoton, Getty Images
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Eddie Howe ya sanar cewar sabon dan wasan da ya dauka Sandro Tonali ya taka rawar gani a wasan sada zumunta da Newcastle ta ci Rangers 2-1 ranar Talata.
Newcastle ta dauki dan kwallon kan fam miliyan 55, wanda ya buga minti 45 a karawar da suka yi a filin wasa da ake kira Ibrox.

Asalin hoton, Getty Images
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Tuni David de Gea ya hakura da Manchester United, bayan kaka 12 a kungiyar da taka leda karo 545 tun lokacin da ya koma Old Trafford karkashin Sir, Alex Ferguson.
Mai tsaron ragar ya yi wasa 190 ba tare da kwallo ya shiga ragarsa ba
Onana ya yi kaka bakwai da rabi a Ajax daga nan ya koma Inter Milan a Yulin 2022, bayan da kwantiraginsa ya kare.

Asalin hoton, Getty Images
RB Leipzig ta dauki matashin dan wasa El Chadaille Bitshiabu daga Paris Saint-Germain, kamar yadda kungiyar da ke buga Bundesliga ta sanar.
Leipzig ta ce dan wasan mai shekarar 18, ya saka hannu kan yarjejeniyar kaka biyar, wadda za ta kare a karshen kakar 2028.
Bitshiabu ya fara yi wa PSG tamaula yana da shekara 19, wanda ke buga wa tawagar Faransa tamaula ta matasa 'yan kasa da shekara 19.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X