Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

'Yan sanda na gudanar da bincike a kusa da fadar shugaban kasar Kamaru

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya, Halima Umar Saleh and Mustapha Musa Kaita

  1. Kamfanin jirgin saman Qantas zai kori ma'aikata 6,000

    Kamfanin jiragen saman Qantas ya ce zai kori mutum 6,000 daga aiki a wani bangare na kokarin da yake yi na magance tabarbarewar tattalin arzikin da ya fada sanadin annobar korona.

    Adadin ya yi daidai da kashi daya cikin biyar na ma'aikatan kamfani gabanin barkewar annobar. A watan Maris ya bai wa kashi 80 na ma'aikatansa hutu saboda cutar korona.

    Kamfanin na kasar Australia ya ce dakatar da sufurin jiragen sama ta yi matukar gigita tattalin arzikinsa da hanyoyin samun kundin shigarsa.

    Makon jiya, gwamnatin Australia ta ce iyakokinta za su ci gaba da kasancewa a rufe watakila zuwa baɗi.

  2. Ghana za ta sake gina ofishin jakadancin Najeriya

    Ministan harkokin wajen Ghana ya ce kasarsa za ta sake gina ofishin jakadancin Najeriya da ke Accra wanda aka rusa.

    A makon da ya wuce ne wasu mutane dauke da makamai suka lalata ginin wanda ba a kammalashi ba.

    Tuni aka damke mutane biyu bisa zargin wannan aika-aikar.

    Ministar harkokin wajen, Shirley Ayorkor Botchwey, ta ce gwamnati za ta gaggauta gyara wuraren da aka rusa a ginin.

    Ta ce za a kuma bai wa ofishin jakadancin Najeriya cikakkun takardun filin.

  3. Ɓangaren APC ya ce taron su Buhari na yau haramtacce

    Wani ɓangare na jam'iyyar APC mai mulki Najeriya ya ce taron da Shugaba Muhammadu Buhari zai halarta na ɓangaren Victor Giadom a yau, haramtacce ne.

    Sanarwar da shugaban APC na riko Ntufam Hilliard Etagbo Eta da Sakataren riko Waziri Bulama suka sanya wa hannu ranar Laraba da almuru ta bayyana cewa "yaudarar" shugaban kasar aka yi ya amince cewa Mr Giadom ne sabon shugaban riko na jam'iyyar.

    "Muna so mu bayyana ƙarara cewa mambobin kwamitin gudanarwa na ƙasa sun yi amannar cewa an bai a shugaban kasa gurguwar shawara ko kuma an yaudare shi ya amince da haramtaccen taron da wani mai suna Victor Giadom ya kira ranar 25 ga watan Yuni, 2020," in ji sanarwar.

    Mai taimaka wa shugaban kan harkokin yada labarai Garba Shehu ne ya sanar da hakan a shafinsa na Twitter ranar Laraba da yamma.

    Masharhanta a Najeriya irin su Dr. Abubakar Kari sun bayyana matakin a matsayin mai cike da ban mamaki da kuma ɗaure kai.Don kuwa a cewarsa: "sanarwar, wani babban al'amari ne kuma tasirin da za ta iya yi yana da girman gaske".

    Ya ce hakan na iya nufin sai dai su Bola Ahmed Tinubu wato jagoran APC na ƙasa da kuma ɓangaren Adams Oshiomhole, shugaban jam'iyyar da aka dakatar, su je su sake shiri.

  4. COVID-19: An soma killace mutanen da suka isa New York daga wasu jihohi

    Wani matakin killace duk mutanen da suka isa New York da New Jersey da Connecticut daga sauran jihohin Amurka takwas mafi fama da annobar korona, tsawon kwana goma sha huɗu, ya fara aiki.

    A New York, inda aka samu raguwar yaɗa cutar korona, an yi barazanar lafta tara mai yawan gaske ga duk mutumin da ya yi kunne ƙashi.

    Jihohin da lamarin ya shafa sun haɗar da Texas da Florida da Carolinas, inda ƙaruwar ɗumbin masu kamuwa da aka samu ya tura alƙaluman masu korona na kullum a faɗin Amurka zuwa kusan wani matsayin da ba a taɓa gani ba.

    An ba da rahoto a jiya Laraba cewa a ƙalla mutum dubu talatin da shida ne suka kamu da cutar a Amurka.

    Ta bayyana cewa gomman jami'an leƙen asiri ne aka buƙaci su killace kansu a Amurka bayan an gano biyu daga ciki sun kamu da korona lokacin da suka halarci gangamin da Shugaba Trump ya yi.

    An ba da rahoto mutanen na cikin ma'aikata shida da suka kamu da cutar lokacin da suke taimaka wajen shirya gangami na Tulsa cikin jihar Oklahoma a wannan mako.

    An dai soki lamirin Mista Trump saboda gudanar da gangami a birnin da ake samun ƙaruwar masu kamuwa da cuta.

  5. COVID-19: Shugaban Senegal Macky Sall ya killace kansa

    Shugaban kasar Senegal Macky Sall ya killace kansa bayan ya yi mu'amala da wani mutum da ya kamu da cutar korona.

    Gwajin da aka yi wa shugaban kasar ya nuna cewa ba ya dauke da cutar amma zai killace kansa tsawon mako biyu a matsayin riga-kafi, a cewar sakon da ofishinsa ya watsa a gidan talabijin na kasar.

    Ranar Laraba 'yar majalisar dokokin Senegal Yeya Diallo ta bayyana cewa ta kamu da cutar korona.

    Ta yi kira ga jama'a su dauki matakan kariya daga cutar irin su tsafta da yin nesa-nesa da juna

    An tabbatar mutum 6,129 sun kamu da cutar korona a Senegal yayin da ta yi ajalin mutum 93.

  6. Barkanmu da safiya

      • Marubuci, Nasidi Adamu Yahya
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Hausa, Abuja

    Nasidi AdamuYahaya ne yake yi muku barka da warhaka.

    Muna fatan za ku kasance tare da mu tsawon wannan rana domin sanin halin da duniya take ciki.

    Za mu kawo muku labarai da rahotannin da suka shafi rayuwarku, musamman kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da makwabtansu, har ma da sassan duniya.