Dubban Iraniyawa na halartar jana'izar Ebrahim Raisi

Wannan shafi ne da ke kawo muku abin da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar 20 ga watan Mayun, 2024.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Muhammad Annur Muhammad

  1. Mutum ɗaya ya mutu, 30 sun ji rauni bayan jirginsu ya haɗu da gargada a sama

    Jirgin sama na Singapore

    Asalin hoton, Getty Images

    Fasinja ɗaya ya mutu wasu sama da 30 sun ji rauni a cikin wani jirgin sama na ƙasar Singapore da zai koma ƙasar daga London bayan da ya gamu da mummunar gargada a sama.

    Sakamakon lamarin an karkatar da jirgin ƙirar Boeing 777-300ER zuwa Bangkok, inda ya sauƙa a can.

    Jirgin mai lamba SQ 321 yana ɗauke da fasinja 211 da ma'aikatansa 18 kamar yadda wata sanarwa da kamfanin jirgin ya fitar.

    Ana can ana ci gaba da kula da wadanda suka ji raunin da taimakon hukumomin Thailand, inda aka tashi wata tawaga ta musamman ta ma'aikatan lafiya daga Singapore din domin ba su kulawa.

    Zuwa yanzu ba a san takamaimai abin da ya faru a cikin jirgin ba bayan da ya gamu da gargadar a sama.

    Abu ne da aka saba jirgi ya gamu da gargada a sama, to amma irin wannan mai tsanani ba kasafai ake haduwa da ita ba.

    Wani lokaci akan iya hasashen gargadar - kuma matuka jirgin sama sukan aika da sako ga takwarorinsu da ke hanya domin gargaɗinsu, to amma kuma matsalar kan faru kwatsam - kuma za ta iya faruwa a ko'ina kuma a kodayaushe.

  2. Tsofaffin ƴansanda na zanga-zanga a Abuja

    Tsofaffin ƴansanda

    Asalin hoton, Channels TV

    Jami'an ƴansandan Najeriya da suka yi ritaya, waɗanda ke karkashin tsarin fansho na karo-karo (contributory pension scheme), suna zanga-zanga a harabar majalisar dokokin ƙasar da ke Abuja.

    Tsofaffin jami'an da suka tattaru a harabar majalisar suna korafi ne a kan rashin biyansu kuɗinsu na fansho na wata da watanni.

    Tsofaffin ƴansandan da ke wakiltar rassansu na jihohi daban-daban suna kokawa da irin wahalar da suke ciki a kan ƙin biyansu haƙƙin nasu da hukumar fansho ta ƙasar ta yi.

    Haka kuma suna kira ga gwamnatin tarayya da ta fitar da su daga cikin wannan tsari na fanshon na karo-karo.

    Ko a watan Satumba na 2021, ƴansanda da suka yi ritaya daga jihohi 27 a Najeriyar sun hallara a majalisar dokokin da ke Abuja, inda suke neman a biya su kuɗin fanshonsu.

  3. Majalisar dokokin Rivers za ta tantance waɗanda ake son naɗawa kwamishinoni

    Gwamna Siminalayi Fubara

    Asalin hoton, RIVERS STATE GOVERNMENT/FACEBOOK

    'Yan majsalisar dokokin Rivers da ke biyayya ga gwamnan jihar, Siminalayi Fubara, za su tantance mutane takwas da gwamnan ya aika sunayensu, domin naɗa su kwamishinoni.

    A wata wasika da akawun majalisar, Dr. G, N Gillis-West, ya aika, a jiya Litinin ya gayyaci mutanen da su bayyana a zauren majalisar a yau Talata, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

    Wasikar ta nuna cewa, majalisar karkashin jagorancin shugabanta na bangaren da ke biyayya ga gwamnan, Victor Oko-Jumbo, na sa ran tantance mutanen zuwa karfe goma na safe.

    Wannan shi ne karo na biyu da bangaren majalisar da ke biyayya ga Fubara zai tantance mutanen da za a nada kwamishinoni tun bayan da majalisar ta rabu biyu - masu biyayya ga gwamna da kuma masu biyayya ga tsohon gwamnan jihar kuma ministan Abuja Nyesom Wike.

    A makon da ya gabata ne majalisar bangaren masu biyayya ga Gwamna Fubara ta tantance tare da tabbatar da babban lauya Dagogo Iboroma (SAN) a matsayin sabon babban lauyan gwamnatin jihar kuma kwamishinan sharia, bayan da Farfesa Zaccaeus Adangor, (SAN), wanda ke biyayya ga Wike ya sauka daga wannan mukami, sakamakon sabanin da ya ya tsananta tsakanin gwamnan da tsohon mai gidansa na siyasa.

  4. Yadda dubban Iraniyawa suka fito jana'izar Shugaba Raisi

    Dubban jama'a na ci gaba da taruwa a shirye-shiryen fara jana'izar Shugaba Ebrahim Raisi wanda rasu a hadarin jirgin sama mai saukar ungulu tare da wasu mutum bakwai ciki har da ministan harkokin waje.

    Za a fara jana'izar ne a yankin Tabriz da ke arewa maso yammacin kasar ta Iran inda hadarin jirgin na helikwafta ya faru ranar Lahadi.

    Tuni dubban jama'a suka fara tururuwa a titinan birnin na Tabriz domin nuna alhininsu ga marigayi shugaban da sauran wadanda suka rasu.

    Ana sa ran binne gawar Shugaba Raisi a mahaifarsa da ke Mashhad, jibi Alhamis.

    Iran

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran

    Asalin hoton, Getty Images

  5. 'Yan bindiga sun sace mutane da dama a Abuja

    'Yan bindiga

    Asalin hoton, Getty Images

    Wasu 'yan bindiga sun kai hari a unguwar Dawaki da ke yankin babban birnin tarayya Abuja inda suka sace mutane 13, amma kuma daga bisani jami'an tsaro sun ceto hudu daga cikinsu bayan sun yi artabu.

    Wani mazaunin yankin ya shaida wa BBC cewa 'yan bindigar sun fara zuwa ne suka sace mutum hudu, amma mutanen suka tsere, daga bisani kuma suka sake kama mutum 13, a harin wanda aka kai ranar Lahadi da daddare

    Bayan sun kama mutanen ne jami'an tsaro suka kai dauki inda suka yi artabu da su a kusa da madatsara ruwa ta Usman Dam, inda suka nasarar ceto mutum hudu daga cikin 13.

    Sai dai kuma wasu rahotannin na cewa mutanen da aka sace sun kai 20.

    Sai dai kuma a wata sanarwa da 'yansanda suka fitar, mai magana da yawun rundunar SP Josephine Adeh ta tabbatar da aukuwar satar mutanen.

    Amma sanarwar da 'yansandan suka fitar wadda a ciki suka ce da hadin kan mafarauta suka yi wa barayin kwanton-bauna a tsaunin Ushafa daga Bwari, ba ta bayyana yawan mutanen da aka sace ba.

    Amma kuma 'yansandan sun ce sun yi nasarar ceto mutanen tare da tarwatsa 'yan bindigar da suka ce sun tsere da raunukan bindiga.

    Sanarwar ta kara da cewa yayin da daya daga cikin wadanda aka ceto yake kwance a asibiti ake masa magani, jami'an na ci gaba da bincike domin gano sauran mutanen da aka sace wadanda suka tsere yayin musayar wuta da barayin.

  6. Yadda dubban mutane suka taru a titunanTabriz don jana'izar shugaba Ebrahim Raisi

    A yau ne ake shirin gudanar da janaizar shugaban Iran, Ebrahim Raisi da ya mutu a hatsarin jirgin sama a ranar Lahadin da ta gabata.

    Ga wani bidiyo da ke nuna yadda jama'a suka taru domin halartar jana'izar.

    Bayanan bidiyo, Dubban mutane akan tituna a Tabriz domin jana'izar Raisi
  7. Iran ta fara zaman makokin kwanaki biyar na mutuwar Shugaba Ebrahim Raisi

    ....

    Asalin hoton, Reuters

    Al'ummar Iran sun fara taruwa a biranen kasar domin nuna girmamawa ga Shugaba Ebrahim Raisi, bayan da ya mutu tare da ministan harkokin wajen a hatsarin jirgin sama a wani yanki mai tsaunuka a arewa maso yammacin kasar ranar Lahadi.

    A jiya Litinin ne babban jagoran addinin kasar, Ayatollah Ali Khamenei ya bayar da sanarwar kwanaki biyar ta zaman makoki. An kuma dakatar jarrabawar daliban makarantun kasar.

    Ana kuma shirye-shiryen zaben sabon shugaban kasa da za a gudanar zuwa ranar 28 ga watan Yuni.

    Da fatan za a kasance da mu yayin da muke kawo muku sabbin labarai daga kasar Iran.

  8. Assalamu Alaikum

    Jama'a masu bibiyarmu a wannan shafi na BBC Hausa da ke kawo muku labarai kai tsaye, muna fatan kun tashi lafi.

    A yau Talata ni Muhammad Annur MUhammad ne zan kasance da ku daga yanzu zuwa wani lokaci.

    Da fatan za ku ci gaba da kasaancewa tare da mu.