Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Isra'ila ta ce ta gano hanyoyin cikin ƙasa 800 a Gaza

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. Gwamnatin Amurka na matsa wa Isra'ila kan kiyaye rayukan Falasɗinawa

    Wasu manyan masu faɗa-a-ji a gwamnatin Shugaba Biden na Amurka na ƙara matsa lamba a kan Isra'ila, yayin da sojojinta ke mayar da hankali kan zafafa hare-haren a kudancin Zirin Gaza.

    Mataimakiyar Shugaban Amurkan Kamala Harris ta nuna damuwa kan irin kashe-kashen farar hula na Falasɗinawa da ake yi.

    Ta ce yayin da Isra'ila ke da 'yancin kare kanta, ana kuma kashe Falasdinawan da ba su ji ba su gani ba. Da take jawabi ga manema labarai a Dubai ranar Asabar, Ms Harris ta bayyana irin asarar rayukan da ake.

    Shi kuwa Sakataren Tsaron Amurka Lloyd Austin, cewa ya yi akwai bukatar Isra'ila ta dinga kare fararen hula, "idan kuma ba haka ba to goyon bayan da take samu zai koma ƙiyayya a faɗin duniya".

  2. Yadda kudancin Gaza ya wayi garin Lahadi

  3. Watsa wa Falasɗinawa takardu daga sama abin kunya ne - Unicef

    Asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya (MDD) UNICEF ya bayyana sako wa Falasdinawa wasu takardu da Isra'ila ke yi ta sama waɗanda ya kunshi batun ba su shawara kan tserewa daga gidajensu a zirin Gaza a matsayin abin kunya.

    Wakilin BBC ya ce "babu wani a Isra'ia da zai iya faɗa wa Falasɗinawa wani wuri da za su je don su tsira, sai dai a tura mutane wajen da babu batun tsira".

    Mataimakin shugaban Hamas, Saleh Al-Arouri, ya ce babu wani sauyi a kan waɗanda aka kama har sai an tabbatar da batun tsagaita wuta na dindindin.

    A martanin da ya mayar, Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce ba za a daina yaƙin ba har sai an kawar da Hamas kwatakwata da kuma dawo da sauran waɗanda aka kama gida.

  4. Maraba

    Barka da hantsin Lahadi tare da fatan mun sake haɗuwa lafiya a shafin labarai kai-tsaye.

    Ku biyo ni Umar Mikail don sanin halin da ake ciki a yaƙin da Isra’ila ke yi a Zirin Gaza.

    Za mu kawo sauran rahotonni daga sassan duniya.