Majalisar Dattijan Najeriya ta tantance ƙarin ministocin Tinubu

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da wasu sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Ahmad Tijjani Bawage and A'isha Babangida

  1. Nijar ta hana fitar da iskar gas zuwa ƙetare

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Jamhuriyar Nijar ta hana fitar da iskar gas zuwa ƙasashen waje har zuwa wani lokaci.

    Gwamnatin ƙasar ta sanar da hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talatar da ta gabata.

    Sanarwar ta ce ya kamata a yi amfani da gas din da ake haƙowa a ƙasar wajen wadata kasuwannin cikin gida, kuma idan aka samu wadatan shi sosai, za a iya neman izini na musamman na fitar da shi zuwa kasashen waje.

    Nijar dai ta saba fitar da iskar gas din ta zuwa makwabciyarta Najeriya.

    • 'Mutane sun wahala a Nijar kuma suna neman wanda za su ɗora wa laifi'
    • Abin da ya sa Rasha ta dakatar da bai wa Turai iskar gas
  2. ‘Yan bindiga sun sace daliban Jami’ar Tarayya ta Dutsinma

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƴan bindiga sun sace kimanin dalibai mata biyar na jami'ar da ke Dutsinma a jihar Katsina.

    BBC ta gano cewa lamarin ya faru ne a cikin dare da misalin karfe biyu a ɗakunan kwanan da dalibai ke kamawa a wajen makarantar.

    Jami'in kula da jama'a na ƴan sanda a jihar, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya shaida wa BBC cewa a halin yanzu sun sami nasarar kama mutum daya da ake zargi da hannun sa a sata da garkuwa da ɗaliban.

    "A halin yanzu kuma muna ƙara faɗaɗa bincike don kama sauran mutane da ke da hannu a wannan aikin."

    • Yadda ƴan bindiga suka hallaka aƙalla mutum 30 a Katsina da Kaduna
    • An ceto wasu daga cikin ɗaliban da aka sace a Jami'ar Tarayya ta Gusau
  3. Netflix zai kawo karshen amfani da manhajar kyauta a Kenya

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Manhajar watsa shirye-shiryen bidiyo wato Netflix ya sanar da cewa zai kawo karshen damar da ya bai wa masu kallo kyauta a Kenya a wata mai zuwa yayin da yake neman hanyoyin samun kudaden shiga a cikin gasar kasuwanci.

    A cikin 2021, Netflix ya bai wa ƴan ƙasar da ke gabashin Afirka damar amfani da manhajar ba tare da biyan kudi ba, suna iya zaɓen kowane irin bidiyo su kalla.

    Wannan wani yunƙuri ne na shiga cikin kasuwannin da ke girma a Kenya.

    A cikin wata sanarwa, Netflix ya ce amfani da manhajar a kyauta ba zai kasance ba daga ranar 1 ga watan Nuwamba.

    Yunkurin ya zo ne watanni bayan da Netflix ya rage farashin biyan kuɗi ga masu amfani da manhajar a Kenya.

    Netflix ya kuma rage ƙimar sa da kashi 37 cikin ɗari yayin da yake ke ƙara samun gasa daga sauran manhajoji kamar su Showmax da DStv.

    • Netflix zai biya ma'aikacin jirgin da zai dauka haya dala 385,000 a shekara
    • Saudiyya ta gargaɗi Netflix kan fina-finan da ke keta dokokin Musulunci
  4. Kanawa suna gudanar da bikin takutaha

    ...

    A yau Laraba ne ake gudanar da bikin takutaha a jihar Kano wato ranar tunawa da suna kan haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad SAW.

    Akasari dai a Najeriya ana bikin murnar zagayowar haihuwar annabi ne amma a Kano, su a ranar suna ake yin biki da taruka duk shekara.

    Tun a farko dai, gwamnan jihar, Abba Yusuf ya ayyana yau, Laraba a matsayin ranar hutu

    A cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida na jihar, Malam Baba Dantiye da ya fitar a Kano.

    Dantiye ya ce gwamnan ya buƙaci jama’a da su yi amfani da wannan damar wajen yin tunani a kan koyarwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama tare da sanya su cikin harkokinsu na yau da kullum.

    Ya kuma buƙaci jama’a da su riƙa yin addu’a domin samun zaman lafiya da ci gaba a jihar musamman ma Najeriya baki daya.

    “Muna addu’ar Allah ya ganar da mu cikin wannan mawuyacin lokaci kuma ya albarkace mu a wannan damina da kuma lokacin noman rani mai zuwa,” inji shi.

    Akasari mutane musamman dalibai su kan yi jerin gwano a kan tituna inda suke rere waƙokin yabon annabi yayin da wasu kuma suke hawan dutse dala.

    • Falalar bikin Maulidin manzon Allah
    • Eid El-Maulud: Wasu hotunan yadda aka yi bikin Maulidi a fadin duniya
  5. An tsige Kevin McCarty daga muƙaminsa na shugaban majalisar dokokin Amurka

    Kevin McCarty

    Al'amura sun tsaya ciki a Majalisar Dokokin Amurka, bayan cire kakakin Majalisar Kevin McCarty, da wasu gungun masu ra'ayin 'yan mazan jiya a jam'iyyarsa ta Republican suka yi.

    Wani ɗan majalisa Matt Gaetz ne ya gabatar da kudurin tsige shi, saboda zarginsa da aiki da 'yan Democrats.

    Yanzu ya zamo kakakin Majalisar wakilan ƙasar na farko a tarihi da aka taɓa tsigewa ta irin wannan hanya.

    Yanzu dai majalisar tana hutu har sai an kaɗa kuri'a a mako mai zuwa kan wanda zai maye gurbinsa.

    • Shugaba Biden na fuskantar barazanar tsigewa
    • Me ya sa Amurka ta ƙi kiran hamɓarar da Bazoum, juyin mulkin soja?
    Kevin McCarty

    Ƴan jam'iyyar ta Republican a majalisar sun shiga ruɗani, saboda rashin sanin wanda zai maye gurbin wanda suka cire.

    Wannan ya kawo karshen tsawon watannin da aka shafe ana ja-in-ja a tsakanin 'yan gani kashenin tsohon shugaban ƙasar Donald Trump, da kuma masu matsakaicin ra'ayi a majalisar.

  6. Majalisar wakilai ta buƙaci jami'an tsaro su ceto ƴan yi wa ƙasa hidima bakwai da aka sace

    ...

    Asalin hoton, TWITTER/@FEMIGBAJA

    Bayanan hoto, ...

    Majalisar Wakilai ta yi kira ga Sufeton ƴan sandan Najeriya, Kayode Egbetokun, da sauran jami’an tsaro da su tabbatar da ganin an sako wasu ‘yan yi wa kasa hidima guda bakwai da ‘yan bindiga suka sace.

    Hakan ya biyo bayan amincewa da kudirin da wani ɗan majalisa daga Akwa Ibom, Unyime Idem da wasu mutane takwas suka gabatar a zauren majalisar a ranar Talata.

    Da yake gabatar da kudirin, Idem ya tuna cewa a ranar 17 ga watan Agusta ne wasu ‘yan bindiga suka sace masu yi wa ƙasa hidima guda bakwai daga jihar Akwa Ibom a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa Zamfara.

    Ƴan bindigar sun buƙaci a biya su naira miliyan 200 kafin su saki ƴan yi wa ƙasa hidiman.

    Idem ya ce wannan abin da ya faru zai iya ɓata ainihin manufar bautan ƙasa (NYSC).

    • An kama mutum 32 da hannu kan satar mutane a hanyar Kaduna-Abuja da harin masallacin Neja
    • DG NYSC: Da gaske za a tura masu yi wa kasa hidima fagen yaƙi?
  7. Mutum 21 sun mutu a hatsarin motar bas a Italiya

    Hatsarin bas

    Asalin hoton, Getty Images

    Akalla mutane ashirin da ɗaya da suka haɗa da ƙananan yara biyu ne suka mutu bayan da wata motar safa ta faɗo daga kan gada, sannan ta kama da wuta, a kusa da birnin Venice na ƙasar Italiya.

    Ministan cikin gida na Italiya Matteo Piantedosi, ya ce bas ɗin mai amfani da gas, na ɗauke da nau'in gas ɗin methane wanda ya sa gobarar ta bazu cikin sauri.

    Ya yi gargaɗin cewa adadin waɗanda suka mutu na iya karuwa.

    Motar na ɗauke da yan yawon buɗe ido, wasu daga cikinsu 'yan Ukraine, wasu yan Jamus.

    Akwai motocin aikin ceto da dama da ke aiki, yayin da fargabar adadin waɗanda suka mutu da kuma jikkata ka iya karuwa.

    Firaiministar Italiya Giorgia Meloni, ta ce tana bin abubuwan da ke faruwa tare da kuma da jajantawa waɗanda lamarin ya rutsa da su.

    • Halin da matasa masu son zuwa Turai ke faɗawa a tsibirin Lampedusa
    • Yadda yarinyar da ke son zama ƴar sama-jannati ta nutse a gaɓar tekun Italiya
  8. Ambaliya ta tafi da sojoji sama da ashirin a Indiya

    Ambaliya

    Ana ci gaba da gudanar da wani gagarumin aikin ceto a Indiya, bayan da gagarumar ambaliya ta yi awon gaba da sojoji sama da ashirin a jihar Sikkim.

    An ba da rahoton cewa motocin sojoji da dama sun nutse bayan da kogin Teesta ya yi cikar kwari, sakamakon ruwan sama marka-marka.

    A cikin wata sanarwa da rundunar sojin ƙasar ta fitar, ta ce ambaliyar ta kuma yi ɓarna a wasu sansanonin soji da ke kwarin Lachen.

    • 'Tamkar ambaliyar tsunami ce ta auka wa birnin Libya'
  9. Assalamu Alaikum

    Masu bibiyar BBC Hausa barkan mu da safiya.

    Ku kasance da mu a wannan shafi na kai-tsaye domin kawo muku labarai da rahotannin abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabtanta da kuma sauran sassan duniya.

    Ahmad Tijjani Bawage da Aisha Babangida ne za su kasance da ku a wannan lokaci.