Adadin mutanen da suka mutu a gobarar dajin Hawaii ya kai 106

Asalin hoton, EPA
Adadin wadanda suka mutu sanadin mummunar gobarar daji a jihar Hawaii, ya kai 106 inda kusan mutum 1,300 suka ɓata ba a gan su ba.
Jami’ai sun su ce, sun gano wadanda gobarar dajin da ta mamaye tsibirin Maui a makon jiya, ta fara shafa inda aka bayyana sunayen mutanen biyu na farko da suka mutu sakamakon gobarar, Robert Dyckman, mai shekaru 74, da Buddy Jantoc, mai shekaru 79, dukkansu daga garin Lahaina.
Gwamnan Hawaii, Josh Green ya ce bisa dukkan alamu za a iya kwashe kwanaki da yawa kafin hukumomi su kai ga tantance adadin wadanda suka mutu sanadin gobarar.
Ya kuma ce hukumomi sun sake gano gawawwakin mutum uku, kuma za a sanar da danginsu nan ba da dadewa ba.
- Wutar daji ta ƙone wani gari ƙurmus a Amurka
- Jiya da yau: Bala'in gobarar dajin da ke addabar duniya




