Rundunar sojin Nijar na zargin Faransa da kashe mata dakaru

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Badamasi Abdulkadir Mukhtar and Rabiatu Kabir Runka

  1. Laberiya ta miƙa wa Saliyo tsohon shugaban ƴan sandanta

    Liberia

    Asalin hoton, AFP

    Hukumomi a Laberiya sun kama tsohon shugaban ƴan sanda Saliyo da ake zargi da shirya kifar da gwamnatin shugaba Julius Maada Bio, tare da miƙa shi ga ƙasar.

    Ministan yaɗa labaran Laberiya, Ledgerhood Rennie ya ce an kama Mohammed Y Toure ne “bayan buƙatar hakan da hukumomin Saliyo suka gabatar, inda suke zargin sa da yunƙurin juyin mulki.”

    Ya ce Laberiya ta yanke shawarar miƙa shi ga Saliyo ne bayan kammala bincike a kan batun.

    Ya kuma yi bayanin cewa sun samu tabbacin cewa za a kare ƴancinsa da duk wani haƙƙi da ya kamata a lokacin sauraron ƙarar a Saliyo.

    Tun a shekarar da ta gabata tsohon jami'in ƴan sandan yake zaune a Laberiya.

    Mista Toure na daga cikin ƴan sandan da Saliyo ta kora daga aiki a 2020, ta kuma tilasta wa wasu da dama yin murabus.

  2. Ƙungiyar tawaye da juyin mulkin sojoji ta ɓulla a Nijar

  3. West Ham ta kammala cinikin Maguire da Ward-Prowse

  4. Likitocin Najeriya sun fasa yin zanga-zanga

    Doctors

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Ƙwarewa ta Najeriya (NARD) ta dakatar da shirinta na gudanar da zanga-zanga a sassan ƙasar.

    A ranar 26 ga watan Yuli ne ƙungiyar ta tsunduma yajin aiki, sakamakon rashin biya mata buƙatunta da suka shafi inganta aiki, da ta ce gwamnatin ƙasar ta yi.

    A baya ƙungiyar ta shirya fara zanga-zangar ne a ranar tara ga watan Agusta a asibitocin gwamnati da ke sassan ƙasar, amma ta dakatar da shirin nata bayan taron gaggawa na shugabanninta.

    Shugaban ƙungiyar, Dr. Emeka Orji, ya shaida wa BBC cewa sun janye aniyar tasu ne bayan tattaunawa da ƴan majalisar dokokin tarayya, waɗanda suka nemi uzurin kwana ɗaya don samar da mafita.

    Wannan dai ba shi ne karo na farko da likitoci a Najeriya ke shiga yajin aiki ba.

    A shekarar 2020 likitocin sun shiga yajin aiki a lokacin da ake ganiyar annobar Corona don neman inganta albashi da sauran haƙƙoƙinsu.

  5. Mutum 11 sun ɓace bayan tashin wuta a wurin yawon shakatawa a Faransa

    France

    Asalin hoton, Getty Images

    Mutum 11 sun ɓace bayan tashin wuta a wani sansanin ƴan yawon buɗe ido da ke gabashin Faransa.

    Ƴan kwana-kwana 80 aka tura garin Wintzenheim da ke kusa da kan iyakar Jamus bayan samun bayanin tashin wuta a wurin.

    Da alama wutar ta tashi ne daga wani gida da matasa masu buƙata ta musamman ke zaune.

    Aƙalla mutum ɗaya aka kai asibiti, an kuma kwashe wasu 17 daga wurin.

  6. Majalisar Dattawa ta miƙa sunayen ministocin da ta tabbatar ga Tinubu

    Tinubu

    Asalin hoton, KANO STATE GOCT/FACEBOOK

    Majalisar dattajai ta tura wa shugaba Bola Tinubu sunayen mutum 45 da ta amince ya naɗa su ministoci, daga cikin mutum 48 da ya nemi ta tantance.

    Mai taimaka wa shugaba Tinubu na musamman kan harkokin majalisar, Abdullahi Gumel ya ce hakan na nufin majalisa ta kammala aikin da ya kamata ta yi game da tantance sunayen ministocin.

    A ranar Litinin Majalisar Dattawa ta kammala tantance ministocin, inda ta sanar da cewa akwai mutum uku da ta jingine tabbatar da su saboda bai wa hukumomin tsaro damar kammala aikin da suke yi a kansu.

    Mutum ukun da majalisa ba ta tabbatar da naɗin nasu ba sun haɗa da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da Sanata Abubakar Danladi da kuma Stella Okete.

  7. Za a ci gaba da tattaunawa kan dambarwar siyasar Kenya

    Kenya

    Asalin hoton, Reuters

    Za a koma tattaunawa tsakanin gwamnatin Kenya da ƴan adawar Azimio da Umoja don kawo ƙarshen bore kan tsadar rayuwa da kuma gyaran dokokin zaɓe.

    Azimo ta jagoranci gagarumar zanga-zanga a cikin watan Maris domin nuna adawa ga gwamnatin shugaba William Ruto don neman canza tsarin gudanarwar hukumar zaɓe da kuma rage tsadar rayuwa a ƙasar.

    Lamarin ya ƙara ƙazancewa bayan gwamnati ta ɓullo da ƙarin haraji a watan Yuli da nufin faɗaɗa hanyar samun kuɗin shiga.

    Babu haƙiƙanin lokacin da aka sanya domin wannan tattaunawa da ake sa ran ɓangarorin za su yi.

    A cikin watannin Afrilu da Mayu, ƴan adawar sun dakatar da zanga-zangar, amma daga baya suka ci gaba da yin ta bayan watsewar zaman tattaunawar sasanci.

  8. 'Yan ci-rani 41 sun mutu bayan tarwatsewar jirginsu a tekun Italiya

    s

    Asalin hoton, AFP

    'Yan cirani 41 sun mutu bayan da jirgin ruwan da suke ciki ya tarwatse a tsuburin Lampedusa da ke Italiya.

    Wasu mutum huɗu - da suka tallake rijiya da baya a hatsarin - sun faɗa wa masu aikin ceto cewa, jirgin nasu ya taso ne daga tashar jirgen ruwa na Sfax a Tunisiya, sannan ya nutse a kan hanyarsa ta zuwa Italiya.

    Fiye da mutum 1,800 ne suka rasa rayukansu a wanna shekara a kokarinsu na shiga Turai daga yankin Arewacin Afirka.

    Hukumomin Tunisiya sun ce tashar jiragen ruwa ta Sfax - wanda ke da nisan kilomita 130 daga tsuburin na Lampedusa - ya zama wata kafa da 'yan cirani ke amfani da ita wajen shiga Turai.

    A baya-baya nan masu gadin teku da ƙungiyoyin agaji sun kuɓutar da mutum 2,000 da suka isa tsuburin Lampedusa.

  9. Guguwa mai ƙarfi ta katse lantarki a kudancin Japan

    Khanun Japan

    Asalin hoton, Getty Images

    Mahaukaciyar guguwa haɗe da ruwan sama mai ƙarfin gaske ta afka wa kudancin Japan, inda ta katse wutar lantarki a gidaje aƙalla 1600.

    Rahotanni na cewa guguwar Khanun ta nufi kudu maso gabashin yankin Kyusu, da ke gabar teku.

    Khanun na tafiyar kilomita 130 cikin sa'a guda, inda hukumar yanayin Japan ta yi gargaɗin fuskantar zabtarewar ƙasa da ambaliyar ruwa, don haka mutanen da ke kwari su gaggauta barin wuraren.

    Japan na shirin yin bikin cika shekara 78 da harin da Amirka ta kai Nagasaki, amma wannan guguwa ta janyo an dakatar da gagarumin bikin, maimakon hakan an buƙaci mutane su yi murna daga gida.

    Can a Koriya ta Kudu ma an yi shirin ko ta kwana, sakamakon hasashen guguwar za ta isa can da safiyar Alhamis.

  10. Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 33 a China

    Doksuri

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumomi a birnin Beijing, sun ce an tabbatar da mutuwar mutum 33 a mummunar ambaliyar ruwan da babban birnin China ya fuskanta a makon da ya wuce.

    Hukumomin sun ce har yanzu ana neman wasu mutum 18 da ba a san inda suka shiga ba.

    Guguwar dai ta ɗaiɗaita birnin Beijing, inda ta dangana da lalata arewa maso gabashin gundumar Jilin.

    Gwamnatin China ta girke dubban sojoji da jamai'an sa kai a Jilin, daidai lokacin da ake sa ran guguwar Doksuri na gab da isa can, tuni kuma aka kwashe dubban mutanen da ke zaune ayankin.

  11. Assalamu alaikum

    Masu bibiyar mu a shafin BBC Hausa barkan mu da safiyar Laraba.

    Badamasi Abdulkadir Mukhtar da Aisha Babangida ne ke fatan kasancewa da ku.

    Ku kasance da mu domin kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwaɓtanta da kuma sauran sassan duniya.