Sojojin Najeriya sun tarwatsa sansanin IPOB tare da kwato makamai

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza and Ahmad Tijjani Bawage

  1. Najeriya ta sayi allura 50,000 don yi wa dabbobi riga-kafin cutar Anthrax a jihar Naija

    g

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Najeriya ta aike da allurar riga-kafin cutar Anthrax 50,000 zuwa jihar Naija da ke tsakiyar kasar.

    Cikin wani sakon Twitter da gidan talbijin na ƙasar NTA ya wallafa ya ce za a yi wa dabbobi riga-kafin cutar ne a yankin ƙaramar hukumar Suleja da ke jihar.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

    Haka kuma ita ma gwamnatin jihar Naijan ta sayi allurar riga-kafin cutar kusan 40,000 domin gudanar da aikin yi wa dabbobin riga-kafi.

    Dabbobi na gida da na daji na kamuwa da cutar ne idan suka shaƙe ta daga ƙasa wadda ke ƙunshe da ƙwayoyin cutar ko kuma suka ci ciyawa ko shan ruwan da ke ɗauke da ita.

    Dabbobin da suka fi kamuwa da cutar sun haɗa da shanu da tumaki da awaki da kuma barewa.

    Haka kuma likitoci sun ce mutane na kamuwa da cutar a lokacin da suka yi cuɗanya da dabbobin da ke ɗauke da cutar ko kuma suka taɓa wani abu da ya fito daga jikin dabbobin.

    A baya-bayan nan dai hukumomin Najeriya sun bayyana ɓuallar cutar a jihar ta Naija, lamarin da ya sa hukumomin lafiyar ƙasar yin gargaɗi game da cin naman dabbobin da ba su da lafiya.

    Tuni hukumomi a wasu ƙasashe maƙwabtan Najeriya suka ayyana ɓarkewar cutar, kamar Ghana.

    • Mece ce cutar Anthrax kuma ta yaya ake kamuwa da ita?
    • Gwamnatin Ghana ta hana cin nama tsawon wata ɗaya a wani yanki
  2. Gwamnatin Najeriya ta ƙara kuɗin 'makarantun Unity' da fiye da kashi 100

    cx

    Asalin hoton, nigerianfinder.com

    Gwamnatin Najeriya ta bayyana ƙarin kuɗin makaranta da fiye da kashi 100 ga sabbin ɗaliban da za su shiga makarantun sakandiren gwamnatin tarayya da aka fi sani da 'Makarantun Unity' a faɗin ƙasar.

    A yanzu iyayen sabbin ɗaliban za su biya kuɗin makaranta naira 100,000 a maimakon 45,000 da suka biya a shekarar da ta gabata.

    Ma'aikatar ilimi ta tarayar ƙasar ce ta bayyana haka, cikin wata sanarwa da ta aike wa shugabannin makarantun sakandiren gwamnatin tarayyar.

    Sanarwar mai ɗauke da sa hannun daraktar manyan makarantun sakandire ta ma'aikatar Hajiya Binta Abdulƙadir, ta ce iyayen sabbin ɗalibai za su biya naira 100,000 a zangon karatu na farko na wannan shekera.

    Sanarwar ta kuma ƙara da cewa sabon ƙarin kuɗin makarantar zai shafi duka sauran ɓangarori da harkokin makarantar, ciki har da kuɗin kayan makaranta, da na litattafan karatu, da na rubutu, da na wasanni da ƙungiyoyi da sauransu.

    • Dalibai: 'Ba za mu lamunci karin kudin makaranta a jami'oi ba'
    • Abin da 'yan Najeriya ke cewa kan karin kudin DSTV da GOTV
  3. Da gaske tsaka na ɗauke da guba mai kisa?

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyon

    A baya-bayan nan ana ta yaɗa wani bidiyo a kafafen intanet da ke nuna yadda tsaka ke kashe mutane saboda zargin zuba dafi a abinci ko abin sha.

    Shin ko gaske ne wannan labari?

    Sashen Hausa na BBC ya miƙa wannan tambaya ga Dr Zainab Abubakar wata ƙwararriyar likitar dabbobi kuma mai kula da asibitin dabbobi da ke Nyanya a Abuja.

    Wadda kkuma ta ce babu wani bincike da ya nuna tsaka na ɗauke da guba.

    "Ba gaskiya ba ne. Tsaka ba ta ɗauke da guba mai kisa a yawunta ko a jikinta, ba kamar macizai da ke ɗauke da guba ba"

    To sai dai kuma likitar ta ce tsakar na ɗaukar ƙwayoyin cuta a jikinta daga ruwa ko kasa.

  4. Wannan ne mako mafi zafi cikin shekara 50 a Girka

    g

    Asalin hoton, Getty Images

    Masana yanayi na gargain cewa wannan karshen mako shi ne mafi tsanananin zafi a Girka, cikin shekaru 50, inda yanayin a wasu yankunan ya haura maki 45 a ma'aunin celcius.

    Masana sun shawarci mutane su zauna a gida, yayin da masu kashe gobara ke ci gaba da ƙoƙarin kashe wutar daji da ta kama a ɓangarori da dama, ana kuma sa ran samun irin wannan zafi a kudancin Amurka.

    A watan Yuli ne aka samu tsananin zafi mafi muni da ba a taɓa samun irinsa ba har sau uku, inda yanayin a arewacin Atlantika ya ɗara da kusan kashi biyar fiye da hasashen shekara.

    An yi hasashen zafi mafi muni fiye da yadda ake sa ran zai kai har maki 46 a birnin Phoenix na jihar Arizona.

  5. Mutum shida sun mutu a kifewar jirgin ruwa a tekun Morocco

    d

    Asalin hoton, BANGLADESH NAVY

    Wasu baƙin-haure shida sun mutu bayan da jirgin ruwan da suke ciki ya kife ya nutse a abar tekun Morocco.

    Kamfanin dillancin labarai na Igna ya ruwaito cewa jirgin ruwan ya kife kan wasu duwatsu da ke ƙarƙashin teku, yayin da mutum 48 suka tsira da rayukansu.

    Wannan shi ne hatsarin jirgi na baya-bayan nan a jerin hadurran da aka samu a yankin.

    A makon da ya gabata 'yan kasar Senegal 18 ne suka nutse a tekun kudancin garin Dakhla.

    Mutum 13 daga cikin waɗanda abin ya hatsarin na rutsa da su sun fito ne daga garin Rufisque da ke wajen Dakar babban birnin kasar Senegal.

  6. Sallama

    Masu bin mu a wannan shafi, fatan kun yawi gari lafya a wannan rana ta Asabar.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasance da ku a wannan yini domin kawo muku irin labaran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, musamman Najeriya da makwabtan ƙasashe.

    Kuna iya tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa a shafukanmu na sada zumunta.

    Ku biyo mu....