Kotu ta bayar da belin Alhassan Ado Doguwa

Wannan shafi ne da yake kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza and Ahmad Tijjani Bawage

  1. Shugaban sojojin hayar Rasha 'Wagner' ya ce ana yi musu zagon-ƙasa a Bakhmut

    Shugaban sojojin haya

    Asalin hoton, Reuters

    Shugaban ƙungiyar sojojin hayar Rasha Wagner ya ce ba sa samun alburusan da suke buƙata daga Moscow, yayin da take ƙoƙarin karɓe iko da birnin Bakhmut.

    Dakarun Rasha - da suka hadar da na Wagner da sojojin gwamnatin ƙasar - na ƙoƙarin ƙwace iko da birnin wanda ke gabashin Ukraine.

    To sai dai shugaban Wagner Yevgeny Prigozhin ya yi ƙorafi kan rashin alburushi yana mai cewa hakan na faruwa ne saboda watakila matakan da ake bi wajen samar da alburusan masu tsauri ne ko kuma ana yi musu ƙafar-ungulu ne kawai''.

    Dangantaka tsakanin Wagner da Rasha na ƙara yin tsami.

    ƙungiyar Wagner na da dubban dakaru da ke yaƙi a Ukraine - inda aka ɗauki wasunsu aiki kai-tseye daga gidajen yarin da suke ciki - Kuma suna taka muhimmiyar rawa a yaƙin.

    A wani saƙo da ya wallafa ranar Lahadi Mista Prigozhin ya ce tun ranar 22 ga watan Fabrairu aka sanya hannu a kan takardar izinin sayen alburusan, inda aka yi tsammanin kai alburusan birnin kwana guda bayan nan.

  2. Gobara ta ƙone wasu ƙauyuka uku a Jigawa

    Gobara

    Wata mummunar gobara da ta tashi a wasu ƙauyuka uku a cikin ƙaramar Kiyawa a jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta janyo asarar dukiyoyi masu yawa.

    Gobara

    Gobarar ta yi sanadin ƙonewar ɗaruruwan gidaje da amfanin gona da kuma dabbobi masu yawa.

    Gobara

    Al'amarin ya auku ne ranar Lahadi da rana a ƙauyukan Malamawa da Karangiya da kuma Ƙwalele.

    Gobara

    Mutanen ƙauyukan sun kwana a bayan gari saboda gobarar ta ƙone musu gidajensu.

    Gobara

    Rahotonni sun ce an kwashe lokaci mai tsawo kafin a iya kashe wutar sakamakon iskar da ke kaɗawa a kauyukan.

    Gobara
  3. PDP na gudanar da zan-zanga a ofishin INEC da ke Abuja

    ...
    Bayanan hoto, ..

    Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya na gudanar da wata zanga-zanga a shalkwatar hukumar zaɓen ƙasar INEC a Abuja babban birnin ƙasar.

    Shugaban jam'iyyar na ƙasar Iyorchia Ayu, da ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen da aka gudanar gwamna Ifeanyi Okowa na jihar Delta na daga cikin mutanen da suke jagorantar zanga-zangar.

    A wata sanarwar da Ibrahim Bashir ɗaya daga cikin shugabannin jam'iyyar ya fitar a madadin daraktan yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam'iyyar, ya ce daga cikin mutanen da aka gayyata zuwa zanga-zangar sun haɗar da shugaban kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam'iyyar wato gwamnan jihar Akwa Ibom Udom Emmanuel, da daraktan kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam'iyyar wanda shi ne gwamnan jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal.

    “Gwamnonin jihohin Bayelsa da Edo da Adamawa da Bauchi da Taraba da kuma Osun States, sauran su ne tsoffin shugabannin majalisar dattawan ƙasar Sanata David Mark da Sanata Abubakar Bukola Saraki, da kwamitin amintattun jam'iyyar da 'yan majalisar dattawa da na wakilai na jam'iyyar da sauran masu ruwa da tsaki na jam'iyyar na daga cikin mutanen da suka halarci zanga-zangar'', kamar yadda sanarwar ta bayyana.

    Sanarwar ta kuma umarci jami'an da su sanya baƙin tufafi domin nuna ɓacin ransu a zanga-zangar da za su gudanar a Maitama da ke Abuja.

  4. Masu iƙirarin jihadi huɗu sun gudu daga gidan yarin Mauritaniya

    Ma'aikatar harkokin cikin gida ta Mauritaniya ta ce wasu masu iƙirarin jihadi huɗu sun tsere daga wani wani gidan yari a Nouakchott babban birnin ƙasar bayan da suka kashe wani mai gadin gidan yarin.

    Lamarin ya faru ne ranar Lahadi da daddare bayan da aka samu rahotonnin musayar wuta, lamarin da ya yi sanadin mutuwar jami'an gidan yarin biyu, tare da raunata wasu biyu.

    Hukumomi sun tsananta tsaro a harabar gidan yarin tare da ƙaddamar da farauto fursunonin da suka tseren.

    Ma'aikatar cikin gida ta ƙasar ta buƙaci al'ummar ƙasar da su kai duk wani bayanin da zai taimaka wajen kamo fursunonin.

  5. Amurka na jagorantar atisayen soji a Ghana da Ivory Coast

    sojoji

    Asalin hoton, Reuters

    Amurka na jagorantar wani atisayen soji na kwana 15 a ƙasashen Ghana da Cote d'Ivoire.

    Atisayen wanda aka fara ranar 1 ga watan Maris ya ƙunshi sojoji 1,300 daga ƙasashe 30 na duniya.

    Atisayen wanda aka yi wa laƙabi da "Flintlock 2023'' an shirya shi ne da nufin ƙarfafa wa ƙasashen duniya gwiwwa wajen yaƙar ƙungiyoyin ta'addancin tare da haɗin gwiwwa a kan iyakokin ƙasashe.

    Tun shekarar 2005 ne Amurka ke jagorantar atisayen soji a yankin yammacin Afirka duk shekara.

  6. NDLEA ta gana da takwararta ta Pakisatn don magance safarar ƙwayoyi

    Hukumar Hana sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya NDLE ta ce ta gana ta hukumomin ƙasar Pakistan domin gano hanyoyin da za a magance matsalar safarar ƙwayoyi tsakanin ƙasashen biyu.

    A wata sanarwa da jami'in hulda da jama'a na hukuma femi Babafemi ya fitar ƙarshen mako ya ce shugaban hukumar Bugediya janar Buba Marwa mai ritaya ne ya tura tawagar jami’an domin tattaunawar wadda ta gudana a birnin Vienna na ƙasar Austria.

    ''Tattaunawar da ƙasashen biyu kan safarar ƙwayoyin tsakanin ƙasahen biyu ta gudana ƙarƙashin jagorancin hukumar safarar ƙwayoyi ta duniya, ta kuma mayar da hankali ne wajen inganta harkokin sadarwa tare da musayar bayanan sirri tsakanin NDLEA da kuma hukumar hana sha da fataucin ƙwayoyi ta Pakistan’’ kamar yadda sanarwar ta bayyana.

    A ƙarshen ganawar ƙasashen biyu sun cimma matsaya kan yadda za su inganta haɗin gwiwa wajen magance matsalar safarar miyagun ƙwayoyi musamman ƙwayar Tramadol tsakanin ƙasashen biyu.

  7. Zaɓen Najeriya ya gaza cimma tsammanin al'ummar ƙasar - Amurka

    Biden

    Asalin hoton, Getty Images

    Sama da mako guda bayan gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Najeriya, Amurka ta ce zaɓen ya ya gaza cimma yadda 'yan ƙasar suka yi tsammani.

    Hukumar zaɓen ƙasar ta ayyana Bola Ahmed Tinubu na jam'iyyar APC a matsayin wadda ya lashe zaɓen da adadin ƙuri'u 8,794,726, tazarar ƙuri'a kusan miliyan biyu tsakaninsa da Atiku Abubakar na jam'iyyar PDP.

    Atiku mai shekara 76, ya samu ƙuri'a 6,984,520, yayin da Peter Obi na LP - wanda a ƙasa da shekara guda ya tara matasan mabiya- ya bayar da mamaki a takarar inda ya samu ƙuri'a 6,101,533.

    To sai dai Atiku da Obi dukkansu sun yi zargin maguɗi a zaɓen, inda suka sha alwashin ƙalubalantar nasarar Tinubu a kotu.

    A wata sanarwa da Amurkan da fitar ta hannun jakadiyar ƙasar a Najeriya Mary Beth Leonard, ta ce 'yan Najeriya da dama sun fusata game da sakamakon, inda wasu suka riƙa murna kan nasarar da suka samu.

    Sanarwar ta ƙara da cewa “A bayyane take cewa tsarin zaɓen Najeriya da aka gudanarar ranar 25 ga watan Fabrairu ya gaza cimma yadda 'yan ƙasar suka yi tsammani,''

    “Kamar yadda na sha faɗa a baya gabanin zaɓen, Najeriya ta cimma abubuwa masu yawa a tsawon shekaru sama da 20 da ta yi bayan komawa tafarkin dimoraɗiyya, kuma ci gaban da aka samu a fannin zaɓukan ƙasar na daga cikin nasarorin da ƙasar ta cimma''

    “Yan Najeriya sun nuna sadaukarwarsu ga dimokraɗiyya ranar 25 ga watan fabrairu, to sai dai da yawa sun nuna fusata, yayin da wasu da dama suka nuna murna bayan nasarar da suka samu''.

  8. Assalamu alaikum

    Masu bin mu a wannan shafi barkanmu da safiyar wannan rana ta Litinin, wadda Bahaushe ke yi wa kirari da Mande tushen aiki ko da Nasara na tsoronki.

    Abdullahi Bello Diginza ne zai jagoranci wannan shafi da zai riƙa kawo muku irin wainar da ake toyawa musamman a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Kuna kuma iya ziyartar shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawa a kan labaran da muke wallafawa

    Ku biyo mu...