An dage tattara sakamakon zaben shugaban Najeriya zuwa ranar Litinin

Wannan shafi ne da yake kawo maku bayanai kan abubuwan da suke faruwa a faɗin Najeriya game da zaɓen shugaban ƙasa da na majalisar tarayya.

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Buhari Muhammad Fagge, Abdullahi Bello Diginza, Yusuf Yakasai and Nabeela Mukhtar Uba

  1. Rufewa

    Masu bin mu a wannan shafi nan za mu dakatar da wannan shafi namu da muka kwashe wunin yau muna kawo muku labarai da rahotonni kan sakamakon zaben Najeriya.

    Sai kuma gobe idan Allah ya kai mu za mu sake dawo don ci gaba da kawo muku ingantattu kuma sahihan labarai kan zaben Najeriya na 2023,

    A mma kar ku manta za ku iya lekawa shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.

    A madadin sauran abokan aiki Yusuf Ibrahim Yakasai, Nabeela Muktar Uba tare da Abdullahi Bello Diginza ke cewa ku ci gaba da bibiyar sashen Hausa na BBC.

  2. Zaɓen 2023: SERAP ta nemi Amurka ta soke bizar ƴan siyasar da suka haifar da tashin-tashina

    Ƙungiyar SERAP mai fafutukar yaƙi da cin hanci a Najeriya ta buƙaci Shugaban Amurka, Joe Biden, ya ɗauki mataki kan jami'an gwamnatin Najeriya da ƴan siyasa da waɗanda suke taimaka wa wajen rura wutar rikici yayin zaɓen ƙasar na 2023.

    A jiya Asabar ne, al'ummar Najeriya suka kaɗa ƙuri'a domin zaɓen sabon shugaban ƙasa da na ƴan majalisun dokoki na tarayya. Sai dai an samu rahotannin ɓarkewar tashin hankali a wasu jihohin ƙasar.

    Mataimakin Daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare ya nemi Shugaba Biden ya soke takardar izinin shiga Amurka ta duk wani da ake zargi da hannu a tsoratar da masu zaɓe da cin zarafinsu da tashin-tashina a lokacin zaɓen.

    Sannan kuma ya saka takunkumi kan dukiyoyinsu da na iyalansu.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  3. Jam'iyyar PDP na kan gaba jihar Adamawa

    INEC

    Ana ci gaba da tattara sakamakon zaɓe a Yola, babban birnin jihar Adamawa inda hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC take bayyana sakamakon ɗaya bayan ɗaya.

    Jihar Adamawa dai na da ƙananan hukumomi 21 kuma ita ce mahaifar ɗan takarar Shugaban ƙasa a inuwar Jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar.

    Ga sakamakon zaɓen shugaban ƙasa na wasu kananan hukumomin jihar Adamawa

    Karamar hukumar Lamurde

    APC - 3645

    PDP - 9912

    LP - 9744

    PRP - 18

    SDP - 46

    Ƙaramar hukumar Girei

    APC - 8531

    PDP - 17557

    LP - 3749

    NNPP - 254

    Ƙaramar hukumar Numan

    APC - 5115

    LP - 10229

    NNPP - 168

    PDP - 8984

    Ƙaramar hukumar Demsa

    APC - 5746

    LP - 7962

    NNPP - 199

    PDP - 17166

    Ƙaramar hukumar Song

    APC - 10993

    LP - 8506

    NNPP - 1223

    PDP - 20406

    INEC

    Ƙaramar hukumar Shelleng

    APC 6213

    LP 1028

    NNPP 69

    PDP 14765

    Ƙaramar hukumar Toungo

    APC 4163

    LP 651

    NNPP 59

    PDP 7401

    Ƙaramar hukumar Ganye

    APC 10112

    PDP 21672

    LP 1069

    NNPP 191

    Ƙaramar hukumar Guyuk

    APC 5904

    LP 8165

    NNPP 91

    PDP 13942

    Ƙaramar hukumar Mayo Belwa

    APC 13271

    LP 1392

    NNPP 280

    PDP 23479

    Ƙaramar hukumar Fufore

    APC - 12633

    LP - 897

    NNPP - 508

    PDP - 26059

  4. Jam'iyyar LP na kan gaba a jihar Delta

    Delta

    Sakamakon zaben shugaban kasar da ke fitowa daga jihar Delta a yankin kudu maso kudancin Najeriya, wato jihar dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam'iyyar PDP Ifeanyi Okowa ya nuna cewa dan takarar jam'iyyar Labour Peter Obi ne kan gaba.

    Jihar Delta dai na da kananan hukumomi 25.

    Ga sakamakon wasu kananan hukumomi da INEC ta sanar kawo yanzu:

    Aniocha ta arewa:

    APC - 1,146

    LP - 11,678

    NNPP - 138

    PDP - 3,783

    Ika ta arewa maso gabas:

    APC - 1,902

    LP - 8,980

    NNPP - 120

    PDP - 16,696

    Ethiope ta yamma:

    APC - 3,850

    LP - 10,199

    NNPP - 263

    PDP - 5,403

    Oshimili ta arewa:

    APC - 1688

    LP - 14,929

    NNPP - 135

    PDP - 4,796

  5. Jam'iyyar PDP na kan gaba a jihar Bauchi

    A jihar Bauchi da ke arewa maso gabashin Najeriya hukumar zaben kasar reshen jihar ta fara bayyana sakamakon zaben shugaban kasa, da aka gabatar ranar Asabar.

    Kawo yanzu an gabatar da sakamakon kananan hukumomi 11 daga cikin kananan hukumomin jihar 20

    Kuma alkaluman sakamakon sun nuna cewa jam'iyyar PDP ce kan gaba a yawan kuri'un da aka tattara kawo yanzu.

    Ga sakamakon kamar haka:

    Karamar hukumar Warji:

    APC - 11,862

    LP - 185

    PDP- 17,732

    NNPP- 424

    Karamar hukumar Bogoro:

    APC - 4,850

    LP - 6,866

    NNPP - 798

    PDP - 15,156

    Karamar hukumar Dass:

    APC - 10,939

    LP - 705

    NNPP - 397

    PDP - 13,242

    Karamar hukumar Jama'are:

    APC - 8,410

    LP - 22

    NNPP - 3,638

    PDP - 12,535

    Karamar hukumar Dambam:

    APC - 7,588

    LP - 42

    NNPP - 2,586

    PDP - 12,203

    Karamar hukumar Giade:

    APC - 10,382

    LP - 17

    NNPP - 4002

    PDP - 11,977

    Karamar hukumar Darazo:

    APC - 16,070

    LP - 41

    NNPP -1,895

    PDP -17,459

    Karamar hukumar Kirfi:

    APC - 9,599

    PDP -13, 431

    NNPP - 1,544

    LP - 33

    Karamar hukumar Katagum:

    APC - 20,030

    PDP - 22,987

    NNPP - 9,672

    LP- 493

    Karamar hukumar Misau:

    APC - 14,199

    PDP -18,354

    NNPP - 4115

    LP - 48

    Karamar hukumar Ganjuwa:

    APC - 1,3021

    PDP -17,380

    NNPP - 4,287

    LP -222

  6. Wasu daga sakamakon zaɓen shugaban ƙasa a Jihar Kano

    Kano na da ƙananan hukumomi 44

    1-Ƙaramar Hukumar Ƙaraye

    Mai bayyana sakamako shi ne Dr. Mukhtar Musa

    Jumullar masu kaɗa ƙuri'a: 82,692

    Waɗanda aka tantance: 31,134

    APC - 10,874

    LP - 134

    NNPP - 16,295

    PDP - 2,132

    Jumullar ƙuri'a masu kyau da aka kaɗa: 29,921

    Kuri'un da suka lalace: 723

    Jumullar ƙuri'un da aka kaɗa: 30,644

    2- Ƙaramar Hukumar Garun Mallam

    Jumullar masu kaɗa ƙuri'a: 74,846

    Waɗanda aka tantance: 26,692

    APC - 8,642

    LP - 169

    NNPP - 12,249

    PDP - 4,409

    3- Ƙaramar Hukumar Rimin Gado

    Mai bayyana sakamakon zaɓe: Farfesa Ahmad Iliyasu

    Mazaɓu: 12

    Jumullar masu kaɗa ƙuri'a: 67,128

    Yawan waɗanda aka tantance: 27,476

    Abin da kowace jam'iyy ta samu:

    APC - 10,861

    LP - 76

    NNPP - 14,634

    PDP - 907

    Jumullar ƙuri'a masu kyau: 26,832

    Waɗanda suka lalace: 508

    Jumullar waɗanda aka kaɗa: 27,340

    Matsalolin da aka samu sun hada da kaɗa ƙuri'a sama da ɗaya da neman tayar da hatsaniya.

    4- Ƙaramar Hukumar Kibiya

    Mai bayyana sakamakon zaɓe shi ne: Dr Ghali Saidu

    Jumullar masu kaɗa ƙuri'a da aka yi wa rijista: 77,929

    Yawan waɗanda aka tantance: 28,228

    Abin da kowace jam'iyya ta samu:

    APC - 10,283

    LP - 70

    NNPP - 16,331

    PDP - 753

    Jumullar ƙuri'u masu kyau: 27,648

    Yawan waɗanda suka lalace : 419

    Jumullar ƙuri'un da aka kaɗa : 28,067

    An soke sakamako biyar saboda zaɓe fiye da sau ɗaya da neman tayar da hatsaniya.

    5-Ƙaramar Hukumar Rogo

    Mai bayyana sakamakon zaɓe: Farfesa Abdullahi Imam

    Jumullar masu rijista: 117,162

    Yawan waɗanda aka tantance: 33,445

    Abin da kowace jam'iyya ta samu :

    APC - 10,403

    LP - 343

    NNPP - 19,587

    PDP - 1,616

    Jumullar ƙuri'u masu kyau: 32,255

    Yawan waɗanda suka lalace: 508

    Yawan waɗanda aka kaɗa: 32,763

    6-Ƙaramar Hukumar Makoda

    Mai bayyana sakamakon zaɓe: Dr. Halima Muhd Isa

    Mazaɓu: 11

    Jumullar masu rijista: 75,487

    Yawan waɗanda aka tantance: 27,724

    Abin da kowace jam'iyya ta samu:

    APC - 12,590

    LP - 40

    NNPP - 12,247

    PDP - 1,099

    Jumullar ƙuri'u masu kyau: 26,195

    Yawan waɗanda suka lalace: 584

    Jumullar ƙuri'un da aka kaɗa: 26,779

    An soke zaɓen rumfuna shida saboda zaɓe fiye da sau ɗaya da neman rikita zaɓen.

    7-Ƙaramar Hukumar Kura

    Mai bayyana sakamako: Habibu Rabiu

    Jumullar waɗanda ke da ƙuri'a: 107,866

    Yawan waɗanda aka tantance: 37,613

    Abin da kowace jam'iyya ta samu:

    APC - 10,929

    LP - 126

    NNPP - 20,406

    PDP - 3,987

    Jumullar ƙuri'u masu kyau: 35,901

    Yawan waɗanda suka lalace: 1,281

    Matsalolin da aka samu sun hada da zaɓe sama da sau ɗaya da neman tayar da hatsaniya.

    8-Ƙaramar Hukumar Minjibir

    Mai bayyana sakamako: Dr. Haruna Isa

    Jumullar masu kaɗa ƙuri'a da ke da rijista: 94,186

    Yawan waɗanda aka tantance: 26,245

    Abin da kowace jam'iyya ta samu:

    APC - 6,777

    LP - 123

    NNPP - 15,505

    PDP - 1,833

    Jumullar ƙuri'u masu kyau: 24,969

    Yawan waɗanda suka lalace: 971

    Yawan ƙuri'un da aka kaɗa: 25,940

    9-Ƙaramar Hukumar Sumaila

    Mai bayyana sakamako: Dr. Isa Yusuf Chammo

    Jumullar masu rijista:111,972

    Yawan waɗanda aka tantance: 40,090

    Abin da kowace jam'iyya ta samu:

    APC - 11,341

    LP - 1,106

    NNPP - 24,307

    PDP - 1,553

    Jumullar ƙuri'u masu kyau: 38,911

    Yawan ƙuri'un da suka lalace: 1,179

    Yawan ƙuri'un da aka kaɗa: 40,090

    10-Ƙaramar Hukumar Dawakin Kudu

    Mai bayyana sakamakon zaɓe: Dr. Hauwa Usman

    Jumullar masu rijista: 162,445

    Yawan waɗanda aka tantance: 52,725

    Abin da kowace jam'iyya ta samu:

    APC - 12,258

    LP - 167

    NNPP - 32,925

    PDP - 3,768

    Jumullar ƙuri'u masu kyau: 50,485

    Yawan waɗanda suka lalace: 1,325

    Jumullar ƙuri'un da aka kaɗa: 51,815

  7. Alƙaluman farko sun nuna PDP ce kan gaba a jihar Gombe

    An fara sanar da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da na 'yan majalisar tarayya daga jihar Gombe da ke arewa maso gabashin Najeriya.

    Sakamakon waɗanda jami'an tattara sakamakon zaɓe suka bayyana ya nuna yawan ƙuri'un da kowace jam'iyya ta samu.

    Ga wasu daga bayanan da muka samu kawo yanzu a zaɓen shugaban ƙasa.

    ƙaramar hukumar Shongam

    APC - 7,525

    PDP - 13,520

    NNPP- 256

    LP - 2,579

    Karamar hukumar Balanga

    APC - 11,715

    PDP - 23,326

    NNPP - 405.

    LP - 3,760

    Karamar hukumar Nafada

    APC- 8,242

    PDP-12,339

    NNPP-344

    LP- 7

    Karamar hukumar Funakaye

    APC - 12,672

    PDP - 25,384

    NNPP - 767

    LP - 320

    A ɓangaren zaɓen ƴan majalisar dattijai ma babban jami'in tattara sakamakon zaɓe a mazaɓar Gombe ta Arewa ya bayyana sakamakon zaɓen.

    Dokta Muhammad Umar ya bayyana sakamakon kamar haka:

    PDP - 22,689

    APC - 17,739

    NNPP - 959

    LP - 70

    Sakamakon dai ya nuna cewa jam'iyyar PDP ce ta samu nasara.

    Jami'in ya kuma bayyana sakamakon zaben majalisar wakilai ta tarayya ta mazaɓar ɗan majalisar tarayya ta Kwami/Gombe/Funakaye, kamar haka;

    PDP - 21327

    APC - 18550

    NNPP - 1698

    LP - 60

  8. Bola Tinubu na APC ya yi nasara a jihohi 12

  9. An dage tattara sakamakon zaben shugaban Najeriya zuwa ranar Litinin

    INEC

    Shugaban hukumar zaben Najeriya Farfesa Mahmood Yakubu ya dage zaman tattara sakamakon zaben shugaban kasar zuwa ranar Litinin.

    Farfesa Mahmood ya bayyana hakan ne bayan gabatar da sakamakon jihar Ekiti a zauren tattara sakamakon zaben shugaban kasar da ke Abuja babban birnin kasar.

    Shugaban na INEC ya ce kasancewar jihar Ekitin ce kadai ta kai sakamakonta zuwa zauren tattara sakamakon zuwa yanzu, hukumar ta dage karbar sakamakon zuwa ranar Litinin da misalin karfe 11:00 na safe.

  10. INEC ta fara karɓar sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da jihar Ekiti

    Jihar Ekiti da ke kudu mao yammacin Najeriya ta kasance jiha ta farko da ta fara gabatar da sakamakonta na zaben shugaban ƙasar da aka gudana ranar Asabar 25 ga watan Fabrairu.

    Shugaban hukumar zaben Farfesa Mahmood ya bayar da dama ga babban jami'in haɗa sakamakon zabe a jihar ta Ekiti domin gabatar da sakamakon a zauren tattara sakamakon dake Abuja

    Babban jami’in lura da zaben jihar ta Ekitin ne ya jagoranci gabatar da sakamakon kamar haka:

    APC - 201494

    PDP - 89554

    LP - 11397

    NNPP - 264

    SDP - 2011

    Sakamakon ya nuna cewa jami'iyyar APC ce ta samu nasara a zaɓen na jihar Ekiti.

    Sai dai babban jami'in hada sakamakon zaɓen ya ce an soke zabe a wasu mazaɓu biyu saboda wasu matsaloli guda biyu da suka hadar da:

    Tangardar na'urar BVAS

    Da kuma samun adadin mutanen da suka kada kuri'a a mazabar ya zarta adadin mutanen da na'uar BVAS ta tantance

    JIhar Ekiti
  11. Rundunar ƴan sandan Legas ta cafke ƴan banga sama da 20

    Rundunar ƴan sandan Najeriya a jihar Legas ta ce ta kama fiye da ƴan bangar siyasa 20 bisa hannu a rikicin zaɓe da satar akwatin zaɓe a wasu sassan jihar yayin babban zaɓen shugaban ƙasa da na ƴan majalisar dokoki da aka yi ranar Asabar.

    Kakakin rundunar, Benjamin Hundeyin, ya ce rundunarsu ta amsa kiraye-kirayen waya daga rumfunan zaɓe 13,325 a Legas.

    Hundeyin, wanda ya tabbatar da hakan a hirar da ya yi da gidan talabijin na Channels, ya bayyana tashin hankalin da ya faru a Okota da Mafoluku da Oshodi da Elegushi da sauran yankunan jihar a matsayin bangar siyasa tsagwaronta.

    Ya kuma tabbatar cewa ƴan bangar sun kutsa kai wuraren, inda suka tarwatsa tsarin zaɓen.

  12. INEC ce kawai ke da alhakin bayyana sakamakon zaɓe - Mahmood

    shugaban zabe

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar zaɓen Najeriya ta gargaɗi jam'iyyun siyasa kan yaɗa sakamakon zaben shugaban ƙasar da na 'yan majalisun dokoki na tarayya.

    Shugaban hukumar Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a lokacin ƙaddamar da buɗe zauren tattara sakamakon zaɓen shugaban ƙasa a Abuja babban birnin ƙasar.

    Farfesa Mahmood ya ce hukumar INEC ce kawai doka ta ɗora wa alhakin fitar da sakamakon zaɓen.

    “Ina kira ga jam'iyyun siyasa da kafofin yaɗa labarai da su ɗauki alkaluman sakamakon daga sakamakon da muka sanar, a matsayinmu na waɗanda doka ta ɗora wa alhakin fitar da alkaluman sakamakon zaɓen'', in ji Farfesa Mahmood.

    A jiya Asabar ne dai hukumar ta gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na 'yan majalisun dokoki na tarayya.

    Hukumar na gargaɗin ne a daidai lokacin da sakamakon zaɓukan ke ci gaba da fitowa.

  13. Bola Tinubu na APC ya samu nasara a jihar Ekiti, Umar Shehu Elleman, Lagos

    An kammala tattara sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da na ƴan majalisar dokoki na jihar Ekiti da aka kaɗa a jiya Asabar.

    Jihar ta kuma kasance jiha ta farko a kudu maso yammacin Najeriya da ta sanar da sakamakon zaben bayan kammala tattara su.

    Sakamakon da hukumar zaɓe INEC ta bayyana ya nuna cewa Bola Tinubu ya samu kashi 65.38% na ƙuri'un da aka kaɗa sai Atiku Abubakar na PDP da ya samu kashi29.06% na ƙuri'unyayin sai ɗan takarar Jam'iyyar Labour Peter Obi ya tashi da kashi 3.7% yayin da Rabiu Kwankwaso na NNPP ya samu kashi 0.09%

    Sai dai har yanzu sauran jihohin na dakon a gama tattara alkaluma tare da kawo su kafin a bayar da sanarwar a nan gaba.

    Wakilinmu Umar Shehu Elleman ya ruwaito cewa a kudu maso kudancin ƙasar, ana ci gaba da gudanar da zaɓe a wasu yankuna na jihohin Bayelsa da Kuros-Riba da kuma Edo sakamakon cewa a jiya an samu akasin gudanar da su.

    Gaza gudanar da zaɓen a jiya ya faru ne sakamakon rashin zuwan kayan zaɓe a kan lokaci.

    An kuma samu rahoton tarwatsa masu zaɓe da tayar da rikici da 'yan bindiga suka yi a wasu mazaɓu a jihar Legas a jiya, inda aka kuma raunata wata mata a rumfar zaɓe a Surulere wadda a halin yanzu take asibiti.

  14. Buhari ya jajanta wa waɗanda gobara ta ƙona wa shaguna a Maiduguri

    Presidency

    Asalin hoton, NIGERIA PRESIDENCY

    Shugaba Muhammadu Buhari ya jajanta wa waɗanda gobara ta ƙona wa shaguna a babbar kasuwar Maiduguri ta Monday Market da ke jihar Borno.

    A cikin wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kan harkokin yaɗa labarai, Mallam Garba Shehu ya fitar, shugaban ya yi kira ga mutane su riƙa kula tare da yin taka tsan-tsan.

    Buhari ya ce ya kamata mutane su ƙara kula a wannan lokaci da ake samun yanayi na iska saboda barazanar haddasa gobara a dazuka da gidaje da gine-ginen mutane da kuma kasuwanni.

    Shugaba Buhari ya yaba da agajin gaggawa da gwamnan jihar Farfesa Babagana Zulum ya bai wa 'yan kasuwar da shagunansu suka ƙone, inda ya bayar da umarni ga dukkan hukumomin tarayya da na jiha wajen ganin an taimaka wa mutanen.

    Ya kuma buƙaci hukumomin kashe gobara su tabbata suna shirye a kowane lokaci don ganin sun takaita afkuwar gobara da ake samu a kasuwanni da kuma sauran bala'o'i.

  15. Zaɓen 2023: Da gaske ne an yi wa rumbun INEC kutse don maguɗin zaɓe?

    Hoton na'urar INEC
    Bayanan hoto, BBC ta gudanar da bincike a kan zargin amfani da na'urar tantance masu zaɓe don maguɗi

    Magoya bayan ƴan hammaya a zaɓen Najeriya a shafukan sada zumunta da muhawara suna zargin cewa mutane sun yi kutse a shafin hukumar zaɓen ƙasar inda suke sanya sakamakon zaɓe na ƙarya.

    An samar da wata kafa a shafin hukumar zaɓen, inda za a iya ganin sakamakon zaɓen da hukumar ke sanya wa kai tsaye.

    Sai dai shafin da ake zargin cewa an yi kutsen ana sanya sakamako na ƙarya, ba ainahin shafin INEC ba ne, shafi ne shi kansa na bogi wanda aka ƙirƙira aka kuma tsara, ta yadda ya yi kama da na hukumar, kuma ake ta yaɗa shi.

    Nazarin da sashen binciken ƙwaƙwaf da tantance labaran gaskiya daga na bogi na BBC, wanda ya gano hakan, ya yi, ya kuma gano cewa shi kansa adireshin shafin na bogi ba ɗaya yake da na hukumar zaɓen ba, sannan yana tattare da kura-kurai kamar yadda aka saba gani a yawancin shafuka na bogi.

    A dangane da haka za a iya cewa ba wata shakka ko alama a yanzu ba wani kutse da aka yi wa shafin hukumar zaɓen Najeriyar, kamar yadda da dama wasu suke yarda.

    Bayan wannan ma akwai kuma wasu rahotannin da ake ta yaɗawa cewa, INEC ta yi amfani da na'urarta ta tantance masu zaɓe wajen yin maguɗi, inda ake ta yada waɗannan labarai a shafukan sada zumunta na muhawara.

    Wannan ne ma har ya sa wasu magoya bayan 'yan hamayya ke barazanar tayar da tarzoma idan dan takararsu bai ci zaɓe ba.

    To amma gaskiya ne cewa na'urar ta kasa aiki a wasu wuraren zaɓen a ƙasar saboda wasu matsaloli nata ko kuma rashin intanet.

    Wasu fitattun masu amfani da shafukan sada zumunta na yaɗa cewa hukumar zaɓen ƙasar da kuma jam'iyya mai mulki APC za su yi maguɗi a zaɓen na 2023, wanda hakan ke sanya shakku a kan 'yancin-kai da kuma gaskiyar hukumar.

  16. Ana zaɓe a jihar Bayelsa

    BBC

    Ana kaɗa ƙuri'a a zaɓukan da aka dakatar a wasu yankuna ranar Asabar a jihar Bayelsa.

    An buɗe rumfuna uku kuma tuni aka sanya masu zaɓen cikin layi domin su fara kaɗawa.

    BBC
  17. An cinna wa ofishin INEC na Takai wuta a Kano

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar ƴan sanda a jihar Kano ta tabbatar da cewa an cinna wa ofishin hukumar zaɓe ta ƙasar reshen ƙaramar hukumar Takai wuta.

    Kakakin rundunar SP Abdullahi Haruna kiyawa ne ya tabbatar wa da BBC faruwar lamarin.

    'Ƴan banga ne suka cinna wa janareton da ake aiki da shi a cibiyar wuta, lokacin da suka shiga wajen ta baya, amma ba wani ci ta yi ba, kuma an kashe ta, tuni muka ƙara yawan jami'anmu a wajen,' in ji kakakin.

    BBC ta tuntuɓi wani ganau wanda ya ce an cinna wutar kuma ta ƙona wasu robobi da aka zuba takardun ƙuri'un da aka kaɗa amma ba ta ƙona wajen da ake aikin ƙirga ƙuri'u ba.

  18. Labarai da dumi-dumi, INEC ta ƙaddamar da zauren tattara sakamakon zaɓen shugaban ƙasa

    National Collation Centre

    Asalin hoton, INEC

    Shugaban Hukumar Zaɓen Najeriya, Farfesa Mahmood Yakubu ya ayyana buɗe zauren karɓar sakamakon zaɓen shugaban ƙasa na 2023 a hukumance.

    Shugaban na INEC ya ce za a fara tattara sakamakon ne daga gundumomi zuwa ƙananan hukumomi, daga nan sai a kai matakin jiha.

    Ya ce bayan nan ne kuma za a kai sakamakon zuwa Abuja, babban birnin tarayya, a zauren tattara sakamakon.

    Yakubu ya ce baturen zaɓe idan ya zo sanar da sakamakon zaɓen jihar da ya zo da ita, zai faɗi ta yadda kowa zai ji, inda zai faɗi yawan mutanen da aka yi wa rajista da waɗanda suka samu damar kaɗa kuri'a da kuma kuri'un da suka ɓaci.

    Shugaban na INEC ya ce bayan haka baturen tattara sakamakon zaɓen kowace jiha zai faɗi yawan kuri'un da kowace jam'iyya ta samu, sannan sai a kira wakilan jam'iyya su zo su sanya hannu idan suka amince da sakamakon.

    Shugaban na INEC ya yi kira ga dukkan wakilan jam'iyyu da kuma 'yan jarida da su tabbatar da cewa sakamakon zaɓen da hukumar ta sanar kaɗai za su yaɗa.

    Ya ƙara da cewa babu wani wuri da ake sanar da sakamakon zaɓen illa babban zauren da aka tanada.

    Yanzu dai an tafi hutun har zuwa karfe shida na yamma lokacin da za a dawo domin fara sanar da sakamakon zaɓen shugaban ƙasar gadan-gadan.

    National Collation Centre

    Asalin hoton, INEC

  19. Kwanana ɗaya da wuni guda ban ci komai ba, in ji ma'aikacin INEC na wucin-gadi

    BBC

    Wata matsala da ake fuskanta a jihar Kano ita ce ta rashin biyan ma'aikatan INEC na wucin-gadi kuɗaɗensu na alawus.

    Wani da BBC ta zanta da shi ya ce tun daga lokacin da suka fara karɓar horo kan wannan aikin, ba a ba su komai ba, kuma sai da suka kwashe kwana biyu suna barci a kan benci.

    "Kwanana ɗaya da yini guda ban ci komai ba, babu wanda ya kawo mana ko da ruwan sha balle maganar kuɗin mota, kuɗi muka ara muka zo nan.

    "Da muka zo nan an faɗa mana ana bayar da alawus na dubu huɗu amma a yanzu cikin ƙasa da awa guda an ce wai an koma bayar da 3,500, an rage ɗari biyar," in ji wani ma'aikaci da BBC ta zanta da shi.

    Duk da cewa sunayensu na cikin jerin waɗanda za su yi zaɓen gwamna, amma ya ce shi ba zai yi wannan aiki ba a lokacin zaɓen gwamna mai zuwa.

    Sai dai, mun tuntuɓi wata jami'ar hukumar ta INEC Zainab Aminu Abubakar domin ji daga gareta, inda ta ce ba ta da masaniya a kan wannan magana, amma ta ce za su yi bincike kan lamarin.