Isra'ila ta kai hari ta sama zuwa Syria

Asalin hoton, Getty Images
Kafafen yaa labaran Syria sun ce Isra'ila ta kai wani farmaki ta sama a babban birnin kasarta, Damascus.
Sojojin Syria sun ce akallam mutum biyar ne suka mutu bayan harin na ranar Lahadi a birnin Damascus da da kewayansa.
Jami'ai sun ce an lalata wani gini a tsakiyar unguwar Kafr Sousa da ke Damascus, tare da kashe fararen hula huɗu da soja ɗaya.
Ƙungiyar kare hakkin ɗan adam ta Syrian Observatory for Human rights da ke da mazauni a Birntaniya ta ce samamen ya halaka mutum 15 ciki har da farar hula, ya kuma lalata gidaje a birnin.
A cewarta, harin ya shafi wasu wurare da ke kusa da cibiyar al'adu ta Iran.
Kakakin rundunar sojin Isra'ila ya ki cewa komai kan batun.
Amma dai Isra'ila ta sha kai hare-hare kan wurare a Syria da ke da alaƙa da Iran da mayaƙan Hezbollah kuma ba ta cika ɗaukar nauyin hare-haren ba

