Gwamnatin Tarayya ta ba da umurnin sake bude kamfanin simintin Dangote na Obajana

Wannan shafin yana kawo maku labaran da suka shafi Najeriya da makwaftanta da ma wasu sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi and Ahmad Tijjani Bawage

  1. Na amince da takarar Atiku Abubakar - Wike

    Atiku da Wike

    Asalin hoton, OTHER

    Gwamnan Rivers da ke kudancin Najeriya Nyesom Wike ya tabbatar da mubaya’arsa ga Atiku Abubakar a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023.

    Sai dai Wike ya ce yana nan a kan bakarsa cewar dole shugaban jam’iyyar ta Peoples Democratic Party Iyorchia Ayu ya sauka daga muƙaminsa.

    Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa Wike ya tabbatar da haka ne a wani taro da ya yi da ƴan takarar jam’iyyar na jihar Rivers a mataki daban-daban, a garin Port Harcourt, a daren Alhamis.

    Wike ya ce ana iyakar bakin ƙoƙari wajen ganin an warware rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar sai dai wasu ƴan-ba-ni na-iya ne suke kawo cikas.

    Ya ce “An gama zaɓen fitar da gwani. Na ce a cire ɗan takarar shugaban ƙasa ne?

    Ko na ce a cire ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa? To mene ne kuma ake ba ni haƙuri a kai?

    “Abin da nake cewa shi ne tunda kun samu ɗan takarar shugaban ƙasa to ku ba mu muƙamin shugaban jam’iyya.”

  2. Barkanmu da Juma'a

    Jama'a barkanmu da safiyar Juma'a. Da fatan an tashi lafiya.

    Ku kasance da mu a wannan shafi domin karanta labarai da rahotanni na abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Sunana Haruna Ibrahim Kakangi, kuma ni zan ja ragamar shafin.

    Da fatan za ku je shafukanmu na Facebook da Tuwita da Instagram domin bayyana ra'ayoyinku.

    A Youtube kuma za ku iya bai wa idanunku abinci wajen kallon cikakkun bidiyo.