Macron na shiga tsakani a rikicin Rwanda da Congo

Asalin hoton, Rwanda Presidency
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya gana da shugabannin Rwanda da Jamhuriyar Dimokradiyyar Kongo, yayin da ake ci gaba da samun tashin-tashina a kan iyakarsu kasashen biyu.
Kasashen na Gabashin Afrika na samun rashin jituwa saboda ayyukan yan tawaye a kan iyaka.
Ganawar na zuwa bayan shugaban Rwanda Paul Kagame ya fada a zauren Majalisar Dinkin Duniya cewa, ''nuna wa juna dan yatsa ba zai warware rikici ba''.
Shi kuwa Shugaban Kongo Félix Tshisekedi ya rubuta a shafinsa na Tuwita cewa, ya yadda ya yi aiki da yan tawayen M23, a kokarin ganin sun bar yankunan da suke rike da su, da kuma ganin al'umma sun koma gidajensu.
Shugabannin uku sun yi kebabbar ganawa ce, a wani bangare na babban taron Majalisar Dinkin Duniya da ake yi yanzu haka a birnin New York.
Kongo na zargin Rwanda da goyon bayan kungiyar yan tawayen ta M23, to amma gwamnatin ta shugaba Paul Kagame na musanta zargin.


