A kasar Senegal, a yanzu, mata ne ke rike da kashi 44 na kujerun sabbin 'yan majalisar dokoki da aka zaba.
Bayan zabuka da aka gudanar a watan Yuli, mata ne ke rike da kujerun 'yan majalisa 73 cikin kujeru 165, wanda shi ne kaso mafi yawa a dukkan kasashe da ke yankin.
A fadin Afirka ta yamma, alkaluma mata 'yan majalisa ya bambanta; alal misali a Najeriya, mata na da kashi 4 na kujeru a majalisar kasar, yayin da makwabtanta Niger kuma ke da kashi 26 na mata a majalisar dokokin kasar.
Senegal na mataki na hudu a Afirka sannan na 18 a duniya na 'yan majalisa mata, inda take gaban Switzerland da Faransa da Birtaniya da Amurka, a cewar hukumar 'yan majalisar dokoki na kasashe da ke Geneva.
Wani doka da aka kafa a 2010 da ke son kawo ''daidaiton jinsi'' a dukkan hukumomi, shi ne ya sanya kasar baiwa mata yawan kaso na mukamai a ofisoshi.
A cewar wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya, bayan Senegal, 'yan majalisa 15 ne kadai mata cikin 111 da aka baiwa mukamai ko kujerun ministoci a Afirka ta Yamma da yankin sahel tsakanin watan Disamba zuwa Yuni.
Ga kaso na mata 'yan majalisa da mata ke rike da shi a majalisun dokokin kasashen Afirka ta Yamma
-
Benin kashi 8
-
Burkina Faso kashi 20
-
Cape Verde kashi 39
-
Côte D'Ivoire kashi 14
-
Gambia kashi 9
-
Ghana kashi 15
-
Guinea kashi 30
-
Guinea-Bissau kashi 14
-
Liberia kashi 11
-
Mali kashi 27
-
Mauritania kashi 20
-
Niger kashi 26
-
Nigeria kashi 4
-
Senegal kashi 44
-
Sierra Leone kashi 12
-
Togo kashi 19