Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Fadar Shugaban Najeriya ta yi raddi ga Tinubu

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye na wasu abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Aisha Shariff Bappa and Mustapha Musa Kaita

  1. Daliban Kaduna 701 ba za su rubuta jarrabawar WAEC ba

    Dalibai 701 daga jihar Kaduna da ke arewa maso yammacin Najeriya ba za su zana jarrabawar kammala sakandire ta WAEC ba saboda rashin ba su damar biyan kudaden da ya kamata su biya.

    Jaridar Punch ta ruwaito cewa daliban, wadanda suka fito daga makarantun sakandire daban-daban a jihar an i ba su damar sanya makinsu na makaranta a shafin hukumar da ake shirya jarrabawar kammala karatun sakandiren.

    Ko da yake, hukumar daga bisani ta yi kira ga makarantun da abin ya shafa a kan cewa za a ƙara buɗe shafin domin su sanya makin nasu.

    Makarantun da abin ya shafi ɗalibansu sun haɗa da Government Secondary School Kuse, wadda ɗalibanta da ke ajin karshe 290 abin ya shafa.

    Sai Government Secondary School Independence Way Kaduna, mai ɗalibai 150 da Government Secondary School Kagarko mai dalibai 110 da kuma Government Senior Secondary School Iddah mai dalibai 100.

    Sauran sun hadar da Al-Bahmeen Academy, Kaduna mai dalibai takwas da Kalhyatu AbdulRahman Bin Auf Academy, Jere mai dalibai 15 da Great Panaf Schools Kaduna mai dalibai 13 da ECWA Secondary School, Kubacha mai dalibai 10 sai kuma Government Secondary School Mato mai dalibai biyar.

  2. Fafaroma Francis ya yi wa waɗanda aka kashe a harin coci a Najeriya addu'a

    Fafaroma Francis ya ce zai yi wa wadanda harin cocin Najeriya ya shafa addu'a.

    Rahotanni sun ce an kashe a kalla masu bauta 25 bayan da wasu 'yan bindiga suka kai hari cocin na St Xaviers Catholic Church a ranar Lahadin da ta wuce.

    Harin ya yi matukar tayar da hankalin 'yan Najeriya, in da iyalan wadanda ke ciki ke cikin ɗimuwa.

    Kazalika harin ya sanya fargaba da tsoro a zukatan 'yan Najeriya ciki har da mabiya addinin kirista.

    Wasu hotunan wajen da aka dauka sun nuna jini face face da kuma gawawwakin mutane.

    Tuni dai aka kai wadanda suka ji rauni asibiti inda suke karbar magani a yanzu haka.

    Haka kuma rahotanni sun tabbatar da cewa ba sace limamin coci ko daya daga wajen ba.

    Mutane a sassan Najeriya dai na bayyana matukar damuwa a kan taɓarɓarewar tsaro da kuma yadda har yanzu gwamnati ta kasa magancewa.

  3. Gobara ta lalata komfuta 100 a Kwalejin Ilimi ta Zaria

    Akalla komfutoci fiye da 100 sun ƙone a yayin wata gobara da ta tashi a Kwalejin Ilimi ta gwamnatin tarayya da ke Zaria a jihar Kaduna.

    Jami'an kashe gobara sun dauki dogon lokaci kafin su kashe gobarar wadda ta tashi tun misalin karfe 9 na safiyar Asabar a lokacin da babu kowa a sashen nazarin ilimin komfutar.

    Shugaban kwalejin, Dr Suleiman Balarabe, ya ce gobarar ta tashi ne sakamkon matsala daga wayoyin lantarki.

    Ya ce tuni aka bayar da umarnin kashe duk wasu na'ura da wayoyin lantarki a kwalejin, sannan ya kuma bayar da tabbacin cewa za a kawo sabbin komputoci kwalejin.

    Kazalika ya ce za kuma a dauki mataki na kare afkuwar hakan a gaba.

  4. Koriya ta Kudu ta harba makamai masu linzami takwas a gaɓar tekun gabashinta

    A wani mataki na ramuwar gayya, Koriya ta Kudu ta harba makamai masu linzami takwas a gaɓar tekun gabashinta, a wani atisayen hadin gwiwa da Amurka.

    An harba makaman ne a matsayin martani ga sabon gwajin makamin da Koriya ta Arewa ta yi a karshen mako.

    Rundunar sojan Koriya ta Kudu ta ce tana so ne nuna makwabciyar tata cewa shiru-shiru ba wasa ba ne.

    A ranar Lahadin da ta gabata ma, Pyongyang ta harba makamai masu linzami masu cin gajeren zango guda takwas cikin teku.

    Hakan ya biyo bayan kammala atisayen sojin da Washington da Seoul suka yi a yankin.

  5. An kashe gobarar da ta hallaka mutum 49 a Indonesia

    Hukumar bayat da agajin gaggawa a Bangladesh ta yi nasarar kashe gobarar nan da ta tashi a wani babban wurin ajiya da ke kusa da birnin Chittagong da ke gabashin kasar.

    Sun kwashe awanni talatin suna kokarin shawo kan wutar.

    Akalla mutum 49 da suka haɗa da jami'an kashe gobara goma ne suka mutu.

    Lamarin ya kuma jikkata wasu daruruwan mutane, yayin da da dama suka ɓace.

    Asibitoci a yankin sun cika maƙil, kana ana kira ga jama'a su je su bayar da gudummawar jini don ceto rayukan wadanda yanzu haka suke kwance magashiyyan.

  6. Barkanmu da safiyar Litinin

    Masu karanta labarai a shafinmu na BBC Hausa barkanku da safiya, da fatan wannan rana ta Litinin ta zo mana da tarin albarka.

    Za mu dinga kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye na wasu abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya a yau Litinin.

    Amma kafin nan, a karya kumallo sai a matsao a asha labarai.