Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Fadar Shugaban Najeriya ta yi raddi ga Tinubu

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye na wasu abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Aisha Shariff Bappa and Mustapha Musa Kaita

  1. Sai da safe

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a nan muka zo ƙarshen kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye, sai kuma gobe Talata idan Allah Ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Za ku iya ziyartar shafinmu na Facebook ko Twitter ko kuma na Instagram domin bayyana ra'ayoyinku kan irin labaran da muke wallafawa ko kuma tafka muhawara a kai.

  2. Labarai da dumi-dumi, Boris Johnson ya tsallake rijiya da baya

    Firaiministan Birtaniya Boris Johnson ya tsallake rijiya da baya sakamakon ƙuri'ar yanke-ƙauna da ƴan majalisar Birtaniya suka gudanar.

    Ƴan majalisa 211 ne suka amince ya ci gaba da zama a matsayin firaiminista inda 148 suka yanke ƙauna da shi.

    Shugaban kwamitin masu ra'ayin mazan jiya a majalisar, Sir Graham Brady ne ya sanar da sakamakon zaɓen.

  3. Kotu a Legas ta yanke wa ɗan shekara 73 hukuncin zaman gidan yari na shekara 24

    Wata kotu a Jihar Legas ta yanke wa wani ɗan shekara 73 hukuncin zaman gidan yari na shekara 24 kan laifin almundahana.

    Tun da farko hukumar EFCC da ke yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya ce ta gurfanar da shi a kotu kan zarge-zarge tara ciki har da batun bayar da cakin banki na bogi da satar miliyan 71.

    Ana zarginsa ne da damfarar wani kamfani mai suna Nepal Oil and Gas Services Limited a wani ciniki da ya shafi sayar da wani fili a Onitsha da ke Jihar Anambra.

  4. MDD ta yi gargaɗin cewa Iran na daf da mallakar makamin nukiliya

    Shugaban Hukumar Kula da Makamashin Nukiliya ta Majalisar Dinkin Duniya, Rafael Grossi, ya yi gargadin cewa makwanni ko watanni ne suka rage wa Iran ta kai ga samun isassun kayan da za a iya amfani da su wajen sarrafa makamin nukiliya.

    Mista Grossi ya ce har yanzu Tehran ba ta bayar da wani gamsashen bayani ba kan wasu sinadarin uranium da aka gano a wasu wurare uku da ba ta ayyana a matsayin cibiyoyin makaman nukiliya ba.

    Jami’an hukumar makamashin da ke taro a Vienna za su yi muhawara kan wani kudirin Amurka da manyan kasashen Turai wanda ya buƙaci Iran ta ba hukumar cikakken haɗin kai.

    An dai kasa cimma matsaya a tattaunawar da ake yi da nufin sake farfado da yarjejeniyar nukiliya ta shekarar 2015 wadda ta kunshi sassauta wa Iran takunkuman da aka kakaba mata da nufin rage shirinta na nukiliya.

  5. An kammala shirya dakunan da alhazai za su sauka a Muna lokacin aikin hajji

  6. Mutum 19 sun rasu sakamakon rikici a Yammacin Habasha

    Hukumomi a yammacin Habasha sun lashi takobin tabbatar da an samu zaman lafiya bayan arangamar da jami'an tsaro suka yi da ƴan bindiga, lamarin da ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 19.

    Cikin wanda aka kashe har da wani shugaban gunduma.

    Ganin cewa hankalin duniya ya karkata matuƙa kan yaƙin basasan da ake yi a arewacin ƙasar, an ta samun munanan yaƙe-yaƙe a wasu sassan ƙasar.

    Shugaban ƴan sanda a yankin Benishangul-Gumuz, Harun Umer, ya bayyana cewa ƴan bindiga sun buɗe wuta kan jami'ansa a wani ƙauye mai suna Belo.

    A wani hari da ya biyo baya kuma, ya shaida wa BBC cewa aƙalla mutum 19 aka kashe.

  7. Babu wanda ya isa ya ce shi kaɗai ya ɗora Buhari kan mulki - Fadar Shugaban Najeriya

    Fadar Shugaban Najeriya ta ce babu wanda ya isa ya ce shi kaɗai ya yi uwa ya yi makarɓiya har Shugaba Muhammadu Buhari ya hau kan karagar mulki a zaɓen 2015.

    Mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ne ya fitar da sanarwa inda ya ce abin da ya wuce a baya bai kamata ya zama abin da za a yi la'akari da shi ba a wurin zaɓen da ke tafe.

    Ya bayyana cewa abin da ke da muhimmanci a yanzu shi ne a zaɓi shugaba da zai kawo ci gaba a Najeriya.

    Ya bayyana cewa akwai waɗanda suka ba shugaban shawara da ya ƙara takara da waɗanda suka gina jam'iyya inda ya ce babu wani mutum guda da zai iya cewa shi ya yi duka waɗannan shi kaɗai.

    Sai dai ana ganin wannan sanarwar da Fadar Shugaban Najeriyar ta fitar ba ta rasa nasaba da wasu kalamai da Bola Ahmed Tinubu ya yi masu kama da gori inda ya ce shi ya taimaka Buhari ya ci zaɓe.

  8. ADF sun kashe kusan mutum 20 a Dimokraɗiyyar Kongo

    Rahotanni daga gabashin Jamhuriyyar Dimokraɗiyyar Congo sun ce kusan mutum 20 ne suka rasu a yayin wani hari da aka kai a wani ƙauye.

    Wani jagora a ƙauyen da ƙungiyoyin agaji sun bayyana cewa mayaƙa da ke ƙarƙashin ƙungiyar ƴan tawaye ta Allied Democratic Forces wato ADF sun kashe mazauna ƙauyen tare da ƙona gidaje a ƙauyen Ituri.

    Ƙungiyar ADF ƙungiya ce ta ƴan tawaye a Uganda da ta koma gabashin Kongo a shekarun 1990.

    Wani rahoto na Majalisar Ɗinkin Duniya ya bayyana cewa ƙungiyar ta kashe ɗaruruwan mutane a can.

    Uganda ta tura sojoji zuwa wurin domin taimakawa a yaƙi ADF haka kuma a makon da ya gabata ne ƙasashen biyu suka ƙara tawon wa'adin aikin haɗin gwiwa na samar da tsaro da suka ƙaddamar a bara.

  9. 'Lalacewar tashoshin samar da wutar lantarki 20 ne ya janyo rashin wuta a Najeriya'

    Bayanai sun nuna cewa sakamakon matsalar rashin wutar da ake fama da ita a Najeriya, an gano cewa tashar samar da hasken lantarki 20 ne a kasar suka lalace, abin da ya janyo ake rasa mega wat 2000.

    Najeriya dai na da tashoshin samar da hasken lantarki 23, wanda suke samar da mega watt dubu 11,165.

    Kamfanonin da ke samar da wutar lantarki a kasar ne ke kula da tashoshin.

    Ana dai yawan smaun daukewar wutar lantarki a kai a kai a Najeriya, abin da ke janyo dakushewar harkokin kasuwanci musamman masana'antu da sauransu.

  10. An kashe mutum 20 a Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo

    Rahotanni daga gabashin Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo sun ce an kashe kusan mutum 20 a wani hari da aka kai wani kauye.

    Wani basarake a kauyen da kuma kungiyoyin agaji sun ce wasu 'yan tawaye ne suka kai hari kauyen inda suka kashe mutane tare da kona kauyen da ke kusa da lardin Ituri.

    Kungiyar da ta kai harin ta ADF, ta kasance ta 'yan tawayen Uganda inda daga bisani suka koma zuwa gabashin Congo.

    Majalisar Dinkin Duniya ta rawaito cewa kungiyar 'yan tawayen ta kashe daruruwan mutane a wajen.

    Uganda dai ta tura sojoji dubu 17 zuwa yankin da 'yan tawayen suke domin yakarsu.

  11. Firaministan Birtaniya na fuskantar ƙuri'ar yankan-ƙauna

    Firaministan Birtaniya, Boris Johnson, na fuskantar ƙuri'ar yankan-ƙauna a shugabancinsa na jam'iyyar Conservative.

    Nan gaba a yau ne ake sa ran ƴan majalisa daga jam'iyyar Conservative za su kaɗa ƙuri'a kan ko za su tsige Firaministan daga muƙaminsa.

    Wannan mataki na batun tsige Mr Johnson na zuwa ne bayan ƴan majalisar hamsin da huɗu daga jam'iyyarsa sun rubuta wasika a hukumance suna neman ya sauka.

    Boris Johnson na fuskantar ƙalubale saboda dalilai da dama, da suka haɗa da bayar da izinin gudanar da bukukuwa a gidan Firaminista, yayin kullen korona.

    Akwai ɗan majalisa John Penrose, jagoran yaki da rashawa a gwamnatin Mr Johnson da ya ce ya yi murabus yana mai cewa Firaministan ya saɓa doka.

    Sai dai akwai ministocin gwamnatin Boris Johnson da suka goyi bayansa, ciki har da maitaimakin Firaminista Dominic Raab.

  12. Koriya ta Arewa zata sake gwada makamin nukliya

    Hukumar kula da makamashin Nukiliya ta MDD ta ce Koriya ta Arewa na shirin gudanar da wani gwajin makamin nukiliya.

    Koriyan dai ta taba gudanar da gwajin makamin a 2017.

    Shugaban hukumar makamashin Rafael Grossi,ya ce akwai alamomi da ke nuna an buɗe cibiyar da ake gwajin.

    A shekaru huɗu da suka gabata Koriya ta Arewa ta ce ta rufe cibiyar, wato wurin da take gwajin nukiliya.

    Mista Grossi, ya ce fashewar za ta ci karo da kudurorin kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya,kuma zai haifar da ' babbar damuwa'.

    A tsawon makwanni ana ta fargabar cewa Pyongyang na shirin gudanar da wani gwajin makamin nukiliya.

  13. An kama mutum 11 da kokarin safarar muggan ƙwayoyi masu yawa a filin jirgin saman Abuja da Legas

    Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Najeriya, NDLEA, ta daƙile wani yunkuri na masu safarar muggan kwayoyi a filin jirgin saman Abuja da Legas, inda ta ƙwace kwayoyi da dama.

    Mai magana da yawun hukumar Femi Babafemi, ya ce an kama mutum 11 da ake zargi suna da hannu da safarar lwayoyin.

    A cikin wata sanarwa da ta fitar a jiya Lahadi, NDLEA ta ce an kama wata mata mai nakasa da ta yi kaurin suna wajen safarar kwayoyi mai suna Kasarachi Onumajuru a Umudumaonu da ke yankin Mbaitoli a ranar 29 ga watan Mayun da ya wuce.

    Sanarwar hukumar ta jero sunayen mutanen da ke da hannu wajen safarar kwayoyi, inda mutum na farko shi ne Ofor Chima Chileobi wanda a ranar Jumma'a 20 ga wayan Mayun ya yi kokarin fitar da kwayoyin zuwa Hadaddiyar Daular Larabawa, kuma daga cikin kwayoyin har da wiwi da nauyinta ya kai kilo 30.

  14. Osinbajo da Tinubu sun je Ondo jajantawa waɗanda aka kai wa hari a coci

    Manyan ƴan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyyar APC mai mulki Farfesa Yemi Osinbajo da Bola Ahmad Tinubu sun je jihar Ondo don jajanta wa waɗanda aka kai wa hari a coci a jiya Lahadi.

    Hakazalika Sanata Ibikunle Amosun da Fayemi Kayode waɗanda su ma ƴan takarar ne sun yi wa Ondon tsinke.

    Rahotanni sun ce Bola Tinubu ne ya fara isa sai Amosun da Fayemi, kuma kafin su bar garin shi ma mataimakin shugaban Najeriya Farfesa Osinbajo ya isa.

  15. Mali ta bayyana damuwa kan matakin kungiyar Ecowas

    Mali ta bayyana rashin jin dadinta game da matakin kungiyar Ecowas na ci gaba da sanya mata takunkumin tattalin arziki.

    Ministan harkokin wajen Mali, Abdoulaye Diop, ya shaida wa kafar yada labaran kasar ta ORTM, cewa yana fatan kungiyar za ta ƙara waiwayar lamarin a taron da za ta yi a wata mai zuwa.

    Ecowas ta kara tsawaita matakinta a kan shirin mika mulki a Mali da Guinea da kuma Burkina Faso zuwa 3 ga watan Yuli mai zuwa, bayan taron da shugabannin kasashen kungiyar suka yi a Ghana ranar Asabar.

    Gidan Rediyon RFI na Faransa ya rawaito cewa akwai rarrabuwar kawuna a kan batun gwamnatin rikon kwarya a kasashen uku tsakanin shugabannin Ecowas din.

    A game da batun Burkina Faso, shugabannin kasashen kungiyar sun yi watsi da bukatar Burkina Faso na kasancewa karkashin gwamnatin rikon kwarya har tsawon watanni 36, suna masu cewa ya yi tsawo.

  16. Da gaske mataimakin shugaban ƙasa Yemi Osinbajo ya yi hatsari?

    Mai taimaka wa Farfesa Yemi Osinbajo kan yaɗa labarai Laolu Akande, ya ce ba gaskiya ba ne labarain da aka yaɗa cewa mataimakin shugaban ƙasar ya yi hatsari.

    A yau Litinin ne aka fara yada labarin cewa Farfesa Osinbajo ya yi hatsari a kan hanyarsa ta zuwa jihar Ondo don jajanta wa iyalan waɗanda aka kai wa hari a Cocin Francis a Owo a jiya Lahadi.

    A wani saƙon tuwita da ya wallafa, Akande ya ce mataimakin shugaban ƙasar ya ga wani hatsari ne da aka yi a hanyarsa ta zuwa filin jirgin saman Abuja, inda ya tsaya don ya taimaka wa waɗanda abin ya rutsa da su.

    Ya ƙara da cewa tuni Osinbajo ya isa jihar Ondon don yin abin da ya kai shi.

    "Mataimakin shugaban ƙasar ya ga an yi hatsari a kan hanyarsa ta zuwa filin jirgi da safiyar yau, inda ya tsaya don ya taimaka wajen tsara yadda za a kai mutanen asibiti a motar ɗaukar marasa lafiya ta jerin motocinsa.

    "Daga nan sai ya wuce don tafiyar tasa zuwa Ondon.

    Ita ma hukumar kula da kare afkuwar haɗurra ta Najeriya ta ƙaryata batun cewa Osinbajo ne ya yi hatsarin, kamar yadda aka yi ta yaɗawa a kafafen sada zumunta.

  17. Birtaniya zata aike da makamin roka mai cin dogon zangonta na farko ga Ukraine

    Birtaniya za ta aike da makamin rokarta na farko mai cin dogon zango ga Ukraine domin ta kare kanta duk da barazanar da Rasha ke yi wa kasashen yamma a kan aikewa da irin wadannan makaman.

    Sakataren harkokin tsaron kasar Ben Wallace, ya ce makamin mai suna M270, zai matukar taimakawa Ukraine wajen tunkarar duk wani hari na Rasha.

    Birtaniya ta dauki matakin ne bayan da Amurka ta sanar da cewa za ta aike da nata makaman irin wadannan ga Ukraine a makon da ya wuce.

    Tuni matakin na Amurka ya fusata Rasha, inda har shugaba kasar Vladimir Putin, ya yi barazanar fadada hare-harensa a Ukraine idan har kasashen yamma suka aikewa Ukraine din irin wadannan makamai.

    Baya ga aikewa da makaman, gwamnatin Birtaniyar dai ta kuma ce za a bai wa sojojin Ukraine horo na musamman a Birtaniyar a kan yadda za su yi amfani da makaman da zata aika nan da makonni masu zuwa.

    Mr Wallace, ya ce Birtaniya ce kan gaba wajen aike wa Ukraine makamai don ta kare kanta daga duk wata mamaya ta Rasha.

  18. An kashe wani babban janar ɗin sojan Rasha a Donbas

    Kafar yada labaran Rasha ta tabbatar da kashe daya daga cikin manyan janar din sojan kasar a yayin gwabzawa a gabashin yankin Donbas.

    An kashe Manjo janar Roman Kutuzov wanda shi ne jagoran rundunar da ke yaki a Donesk a wata gwabzawa da ake yi a yankin.

    Har yanzu dai ma'aikatar harkokin tsaron Rashan ba ta ce komai ba kan kisan janar din.

    Ita ma rundunar sojin Ukraine ta tabbatar da kisan janar din, amma ba tare da cikakken bayani a kan yadda laamrin ya faru ba.

    Kisan janar ɗin ya zo ne a dai dai lokacin da ake ta yada jita jita a kafafan sada zumunta cewa an kashe wani janar din Laftanar janar Roman Berdnikov na rundunar ta 29 a karshen mako, ko da yake ba a tabbatar da hakan ba.

    Rasha dai ta tabbatar da kashe mata manyan janar janar uku kawo yanzu, inda Ukraine kuma ke cewa an kashe 12, sai kuma jami'an leken asiri daga kasashen yamma kuma ke cewa mutum bakwai aka kashe.

  19. Ɓarayi ne suka shiga wani rukunin gidaje a Abuja ba masu satar mutane ba - Ƴan sanda

    Rundunar an sandan Najeriya ta babban birnin tarayyar asar Abuja ta ce arayi ne suka shiga wani rukunin gidaje a Unguwar Karsana suka yi sata ba masu satar mutane ba kamar yadda wasu rahotanni suka ce.

    Mai magana da yawun rundunar 'yan sandan Abuja, Josephine Adeh, ta shaida wa BBC cewa "ba 'yan bindiga ba ne, ɓarayi ne kuma ba su saci kowa ba, sai kayayyaki da suka sata."

    Tin da fari rahotanni daga wasu jaridun asar sun ce wani gungun 'yan fashi dauke da makamai ne suka kai hari rukunin gidaje na Efab Queens da ke Karsana Abuja da safiyar yau Litinin.

    Amma wasu mazauna unguwar sun ce wa BBC 'yan fashi wanda akalla sun kai 30 ne suka je rukunin gidajen dauke da makamai inda suka rinka ɓalla ƙofofin gidaje suna shiga.

    Mazauna wajen da BBC ta tuntuba sun ce, 'yan fashin ba su saci kowa ba, sai dai sun saci talbijin da sauran muhimman kayayyaki daga gidajen da suka shiga.

    "Ba su kashe kowa ba, amma sun raunata mutum guda", inji mazauna unguwar, kuma daga baya jami'an 'yan sanda sun je sun fatattake su, ko da yake ba su kama kowa daga cikinsu ba.

  20. An sace mahaifiyar dan takarar sanata a Kano ta tsakiya A A Zaura

    Rahotanni sun ce wasu 'yan bindiga sun sace mahaifiyar dan takarar sanata a Kano ta tsakiya karkashin jam'iyyar APC, Abdulsalam Abdulkarim A A Zaura.

    Lamarin ya faru ne da safiyar Litinin inda 'yan bindigar suka je gidan matar da ke Rangaza a kauyen Zaura a ƙaramar hukumar Ungogo suka sace ta.

    Shugaban ƙaramar hukumar Injiniya bdullahi Garba Ramat, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce jami'an tsaron da ke yanki ne suka sanar da shi.

    Kazalika shugaban karamar hukumar ya rubuta a shafinsa na facebook cewa sun tashi da mummunan labarin sace mahaifiyar A A Zaura.