EU za ta tattauna kan sauya dabarun tsaro a nahiyar

Asalin hoton, Getty Images
A yau ne ministocin kasashen Tarayyar Turai za su gana a Brussels, domin daddale magana guda kan matakin da Turai za ta dauka na tsaron yankin ta hanyar sauya dabaru.
Jami'ai sun ce za a tabo batun zahirin halin da ake ciki kan mamayar da Rasha ta yi wa Ukraine.
Cikin wannan makon ma birnin Brussels na Belgium zai karbi bakun cin taron kungiyar tsaro ta NATO.
Tarayyar Turai na amfani da matakan tsaron tun ma kafin Rasha ta mamaye Ukraine, sai dai jami'ai sun ce tabbas za tattauna kan abubuwan da ke faruwa a zahiri.





