Korona ta sake kama mutum 58 a Najeriya
Hukumar NCDC mai yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a Najeriya ta ce an samu ƙarin mutum 58 da suka kamu da cutar korona ranar Talata.
Jihohin da mutanen suka fito bakwai ne da suka haɗa da Legas (35) da Abuja babban birnin ƙasar (9) da Edo (5) da Delta (4).
Sauran su ne Kano (2) da Rivers (2) da Kaduna (1). Rahoton na NCDC ya nuna babu wanda cutar ta kashe a Talatar.
Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 253,833 ne suka harbu da cutar a Najeriya tun bayan ɓullarta a Fabarairun 2020. Kazalika ta yi ajalin mutum 3,139.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X

